Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Gobara Ta Lakume Shaguna A Kasuwar Argungu

by Muhammad
December 28, 2020
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Argungu
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Jamil Gulma,

Wata gobara da ta tashi tsakiyar daren jiya Lahadi sanadiyyar bugawar wata transfoma da ke bakin babbar kasuwar Argungu da ke jihar Kebbi ta lakume shaguna da kuma rumfunan masu sayarda kayangwari wanda ya yi sanadiyyar hasarar milliyoyin nairori.

samndaads

Daya daga cikin wadanda shagunansu suka money Alhaji Ibrahim Samaila (Aguro) wanda ke da shagon sayarda wayar salula ya bayyanawa wakilinmu da cewa an kira shi ne da misalign karfe daya da rabi na dare sai daya daga cikin yan uwansa ya kira shi ta wayar matarsa sanadiyyar lalacewar layin sa ya gaya shagon sa ya kama wuta.

Lokacin da ya isa wajen ya fatar shagon ba wajen shiga duo da ya ke jama’a sun taru ana ta famar kashe wutar, da ya ke wutar ta ruru sosai ba wanda ke iya shiga kwantenar don fitowa da wadansu kaya saboda haka shagon sa ba abinda aka fitar. Ya ce ya yi hasarar dukiyar da za ta kai kimanin naira milliyan biyar ko fiye.

Ya kuma kara da cewa daman sun dade suka samum barazana daga wannan transfoma saboda sau da yawa ta kan buga sai wuta ta rinka watsi har sai mutane sun watse sannan daga baya jami’an ma’aikatar wuta su zo su gyara, amma dai ba a taba samun irin wannan ba.

Shagunan da suka kone akwai shagon sayarda wayar salula, shagon sayarda kananan tufafi da kayan wasanni mallakar Alfa, shagon Malam Habibu mai sayarda roba, da kuma rumfunan masu sayarda kayangwari sai dai ba rahoton salwantar rayuwa.

Wakilinmu nemi jin ta bakin jami’in hulda da jama’a na hukumar samarwa da kuma raba wutar lantarki ta Kaduna Malam Idris Muhammed amma dai ya ce har wannan lokacin ba su sami wani rahoto ba daga Argungu, sai dai ya ce daman sai jami’an na su sun kammala tattara bayanai kafin su kawo rahoton afkuwar irin wannan lamarin. Ya kuma bayarda tabbacin hukumar za ta yi gaggawar daukar matakan da suka dace don farantawa rayuwar masu huldar da su.

Tuni jami’an kamfanin samarda wutar lantarki da kuma rabawa na Kaduna (KEDCO) sun dukufa wajen gyara transfomar da abin ya faru.

Al’ummar jihar dai suna kokawa kan rashin motocin kashe gobara wanda yanzu haka a karamar hukumar mulki ta Dandi kawai ke da mota daya da shugaban karamar hukumar mulkin ya gyara.

SendShareTweetShare
Previous Post

Akwai Bukatar Matasa Su Zama Jajirtatu Wajen Gina Nijeriya – Amina Muhammad

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Kashe Hakimin Da Suka Sace A Neja

RelatedPosts

Ingantaccen zabe

Aniyar Ganduje Ce Ta Haifar Da Ingantaccen Zabe A Kano – Yusif Ali

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana cewa, kyakkyawar aniyar Gwamna...

Kaduna

Sojoji Sun Yi Wa ‘Yan Bindiga Kwanton Bauna A Kaduna

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Sojojin da ke karkashin ‘Operation Thunder...

Farar Hula

Hankula Sun Tashi A Maiduguri Bayan Babbaka Sojan Da Ya Harbi Farar Hula Hudu

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Mutanen Maiduguri sun shiga tararrabi bayan...

Next Post
Hakimin

‘Yan Bindiga Sun Kashe Hakimin Da Suka Sace A Neja

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version