Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Gobarar Makaranta: Gwamnatin Kogi Ta Wanke Makiyaya

by Muhammad
February 9, 2021
in LABARAI
2 min read
Kogi
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Ahmed Muh’d Danasabe,

Gwamnatin Jihar Kogi a karkashin jagorancin Gwamna Yahaya Bello, ta ce, ko kadan Fulani makiyaya dake zaune a jihar ba su da hannu a kona makarantar sakandiren gwamnati ta GSS Iluke dake yankin karamar hukumar Kabba Bunu a jihar.

samndaads

Wata sanarwa da ta fito daga Kwamishinan Yada Labarai da Sadarwa na Jihar, Mista Kingsley Fanwo, ta kuma ce, gwamnatin jihar ta damu matuka gaya game da bankawa makarantar wuta.

“Gwamnatin jihar ta nuna rashin jin dadinta ganin yadda aka yi gaggawar yanke hukuncin cewa Fulani makiyaya ne suka kona wani bangare ko sashen makarantar. Wannan yanke hukuncin da ba a tabbatar da shi ba kuma dargin yana iya tayar da zaune tsaye a jihar.

“A daidai lokacin da mu ke cigaba da binciken ummul’aba’isan faruwar gobarar, mu na gargadin jama’a da su sanya wa bakunansu linzami a yayin da suke furta maganganun dake fitowa daga bakunan nasu, domin kauce wa abubuwan da za su gurgunta zaman lafiya a tsakanin jama’ar Jihar Kogi da kuma sauran kabilu dake  jihar.

“Jihar Kogi na farin cikin yadda kabilu daban-daban, irinsu Fulani da Bassa da Nupawa da sauransu ke zaune lafiya da junansu, kuma suke harkokinsu ba tare da wata matsala ba a cikin jihar.

“Tuni aka umarci Ma’aikatar Ilimi, Kimiya da Fasaha ta jihar da shugaban karamar hukumar Kabba Bunu da kuma Mai Bai Wa Gwamna Shawara Akan Sha’anin Tsaro da su gaggauta gano dalilin  afkuwar gobarar tare da zakulo wadanda suke da hannu a lamarin komai matsayinsu ko kabilarsu, domin ganin sun fuskanci hukunci daidai da laifinsu.

“Mu na jajenta wa al’ummar Iluke da dukkan wadanda lamarin ya shafa. Mai Girma Gwamnan jihar ta Kogi cikin gaggawa ya bada umarnin gyara makarantar, domin tabbatar da ganin dalibai sun cigaba da karatunsu,” inji sanarwar.

A bangare guda kuwa, kungiyar kare muradin Fulani makiyaya ta kasa (MACBAN) reshen Jihar Kogi, ta gode wa Gwamna Bello a bisa matakan da ya dauka game da zargin da aka yi wa makiyayan.

Kungiyar ta ce, gwamnan ya gudanar da kwakkwaran bincike kuma ya gano cewa ba Fulani makiyaya ba ne suka banka wa makarantar wuta.

“Muna jaddada godiyarmu ga gwamna da kuma mai ba shi shawara akan sha’anin tsaro a bisa gudanar da bincike na hakika,” inji kungiyar a sanarwar da Sakataren MACBAN reshen jihar, Malam Adamu Abubakar, ya sanya wa hannu, inda ya bayyana godiyarsa a madadin kungiyar.

“Muna zaman lafiya a nan Jihar Kogi, ba kamar wasu jihohi ba. Don Allah kada wani ya zo ya haddasa fitina a tsakaninmu,” inji Abubakar.

Daga nan sai ya yi addu’ar Allah ya bai wa Gwamna Yahaya Bello basira, hikima, lafiya da kuma kwarin gwiwar kammala ayyukan da ya faro a jihar.

SendShareTweetShare
Previous Post

Har Yanzu Akwai Kutare Miliyan Biyu A Duniya – Dr. Tsanyawa

Next Post

El-Rufai Ga Gumi: Ka Daina Bata Wa Kanka Lokacin Sulhu Da ’Yan Bindiga

RelatedPosts

Hadiza Usman

Hadiza Bala Usman Ta Yi Ta’aziya Ga Iyalan Marigayi Dikko Inde

by Sulaiman Ibrahim
43 mins ago
0

Daga Abdullahi Sheme A ranar juma'ar da ta gabatane shugabar...

Masana Sun Yaba Wa Shugaba Buhari Kan Sake Nada Hadiza Bala Usman Shugabar NPA

Masana Sun Yaba Wa Shugaba Buhari Kan Sake Nada Hadiza Bala Usman Shugabar NPA

by Sulaiman Ibrahim
51 mins ago
0

Daga Bello Hamza, Abuja Masana da masu ruwa da tsaki...

An Sako Daliban Da Aka Sace A Zamfara

An Sako Daliban Da Aka Sace A Zamfara

by Muhammad
2 hours ago
0

Rahotanni daga jihar Zamfara sun tabbatar da cewa an ceto...

Next Post
Sulhu

El-Rufai Ga Gumi: Ka Daina Bata Wa Kanka Lokacin Sulhu Da ’Yan Bindiga

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version