Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Gobarar Sakkwato: Gwamnatin Tarayya Ta Jajantawa Tambuwal

by Muhammad
January 25, 2021
in LABARAI
1 min read
Hutun Kirsimeti
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga, Sharfaddeen Sidi Umar, Kakkarfar tawagar Gwamnatin Tarayya ta jajantawa Gwamnati da al’ummar Jihar Sakkwato a yau Litinin kan ibtila’in gobarar kasuwar Sakkwato da ta kone a ranar Talatar makon jiya.

Wakilan na Gwamnatin Tarayya sun taho ne a karkashin jagorancin Shugaban Ma’aikata na Fadar Shugaban Kasa, Farfesa Ibrahim Gambari, tsohon Gwamnan Sakkwato, Sanata Aliyu Wamakko, Ministan Sadarwa Ali Isa Pantami, Ministar Ayyukan Jinkai, Sadiya Umar Faruk da Ministan Lamurran ‘Yan Sanda, Maigari Dingyadi.

samndaads

A jawabinsa, Gambari ya bayyyana gobarar a matsayin abin jimami maras misaltuwa wanda ya girgiza Shugaba Muhammadu Buhari matuka a gobarar wadda ba wai kawai za ta shafi ‘yan kasuwa ba, ta kuma taba tattalin arzikin Jiha.

“Shugaban Kasa ya umurce mu da mu zo domin mu jajantawa al’ummar wannan Jiha a madadin Gwamnatin Tarayya kuma a tabbatar maku cewar Gwamnatinsa za ta taimaka domin sake gina kasuwar.”

Da yake jawabi, Gwamna Tambuwal ya godewa Shugaba Muhammadu Buhari kan nuna kulawar gaske tare da turo kakkarfar tawagar domin jajanta masu a lokacin na kalubale.    Ya ce kasuwar ba wai kawai al’ummar Sakkwato ke amfana da ita ba, har da al’ummar kasashen waje.

Ya ce Gwamnatin Jiha za ta himmatu domin sake gina kasuwar da kuma tallafawa ‘yan kasuwar.

Gwamnan ya bukaci Gwamnatin Tarayya da ta sa hannun domin ganin an sake gina kasuwar tare da tallafawa ‘yan kasuwar. Ya ce kasuwar na da shaguna 14, 000, daga baya aka yi karin 2, 000 na wucin gadi wadanda ya ce bakidaya ta na da shaguna 16, 000. Ya ce kashi 60 na kasuwar ya kone bakidaya.

SendShareTweetShare
Previous Post

Ko Akwai Yiyuwar Kyautata Hulda Tsakanin Amurka Da Turai Bayan Sabon Shugaban Kasar Ya Fara Aiki?

Next Post

Shugaban Kasar Sin Ya Yiwa Taron Davos Jawabi Ta Kafar Bidiyo

RelatedPosts

Sarkin Musulmi

Fulani Ba ‘Yan Ta’adda Ba Ne –Sarkin Musulmi

by Muhammad
10 hours ago
0

Mai Alfarma Sarkin Musulmi, Muhammadu Sa’ad Abubakar III, ya ce...

Sulhu Da Masu Garkuwa: Gwamnatin Zamfara Ta Amso Mata Takwas Da ‘Ya’yansu

Sulhu Da Masu Garkuwa: Gwamnatin Zamfara Ta Amso Mata Takwas Da ‘Ya’yansu

by Sulaiman Ibrahim
15 hours ago
0

Daga Hussaini Yero, Gusau A shirin Gwamnatin Jihar Zamfara na...

Gwamnatin Zamfara Ta Amshi Tubabbun ’Yan Bindiga Uku

Gwamnatin Zamfara Ta Amshi Tubabbun ’Yan Bindiga Uku

by Sulaiman Ibrahim
15 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya Gwamnan Jihar Zamfara, Bello Mohammed, Matawallen...

Next Post
Shugaban Kasar Sin Ya Yiwa Taron Davos Jawabi Ta Kafar Bidiyo

Shugaban Kasar Sin Ya Yiwa Taron Davos Jawabi Ta Kafar Bidiyo

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version