Gobe Za A Tsunduma Yajin Aiki, An Gaza Cimma Matsaya Tsakanin Gwamnati Da NLC
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gobe Za a Tsunduma Yajin Aiki, An Gaza Cimma matsaya Tsakanin Gwamnati Da NLC

byAbubakar Sulaiman
1 year ago
NLC

Bayan ganawar sa’o’i huɗu da shugabannin majalisar dokoki da yammacin yau Lahadi a Abuja, ƙungiyar ƙwadago ta tabbatar da cewa za a gabatar gudanar da yajin aiki kamar yadda aka tsara a fadin ƙasar nan a ranar Litinin 3 ga watan Yuni, 2024.

Shugaban ƙungiyar ƙwadago (TUC) Festus Osifo ya bayyana cewa, matakin yajin aikin yana nan tsayin daka, kuma za su gabatar da koken Majalisar ga sassan ƙungiyarsu daban-daban, amma yajin aikin zai fara kamar yadda aka tsara.

  • NLC Na Gudanar Da Zanga-zanga A Ofishin KEDCO Na Kano Kan Ƙarin Ƙuɗin Wutar Lantarki
  • Mafi Ƙarancin Albashi: NLC Za Ta Tsunduma Yajin Aiki

Taron dai ya ƙunshi manyan mutane irin su shugaban majalisar dattawa Godswill Akpabio da kakakin majalisar wakilai Tajudeen Abbas, waɗanda suka yi yunƙurin hana ƙungiyoyin shiga yajin aikin saboda mummunan tasirin da zai iya yi ga al’umma da tattalin arziki Nijeriya.

Rikicin da ke tsakanin gwamnatin tarayya da ƙungiyoyin ya samo asali ne daga taƙaddamar sabon mafi ƙarancin albashi na ƙasa da kuma ƙarin kuɗin wutar lantarki da aka yi a baya-bayan nan. Ƙungiyoyin ƙwadagon dai sun buƙaci a ƙara musu sabon mafi ƙarancin albashin ma’aikata, suna masu cewa ₦30,000 da ake biya a yanzu bai wadatar ba kuma ba dukkan gwamnoni ne ke biyan hakan ba.

 

Ƙungiyoyin dai sun tsayar da ranar 31 ga watan Mayu domin gwamnati ta amince da sabon mafi ƙarancin albashi, amma tattaunawar ta ci tura, lamarin da ya kai ga ayyana yajin aikin.

Ƙungiyoyin sun yi watsi da tayin da gwamnati ta yi masu da dama, ciki har da na baya-bayan nan na ₦60,000, inda suke neman sabon mafi ƙarancin albashi na ₦497,000.

Haka suna son a duba cikar yarjejeniyar mafi ƙarancin albashin ma’aikata a halin yanzu, wanda ba a sake duba shi ba kamar yadda dokar ƙasa ta tanada na tsawon shekaru biyar a ƙarƙashin dokar mafi ƙarancin albashi na shekarar 2019.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwamitin Shura Na Kano Ya Dakatar Da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi
Da ɗumi-ɗuminsa

Kwamitin Shura Na Kano Ya Dakatar Da Malam Lawan Triumph Daga Yin Wa’azi

October 1, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025
Da ɗumi-ɗuminsa

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu
Da ɗumi-ɗuminsa

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Next Post
Taron Karawa Juna Sani Kan Wayewar Kan Kasar Sin Ta Zamani Ya Bukaci Karin Nasarori A Fannin Ilimi

Taron Karawa Juna Sani Kan Wayewar Kan Kasar Sin Ta Zamani Ya Bukaci Karin Nasarori A Fannin Ilimi

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version