Gombe Ta Hau Mataki Na 6 A Rahoton BudgetIT Na Alkinta Dukiyar Al'umma
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gombe Ta Hau Mataki Na 6 A Rahoton BudgetIT Na Alkinta Dukiyar Al’umma

bySulaiman
2 years ago
BudgetIT

Jihar Gombe ta samu nasara a kididdigar kasafin kudi na 2023 wadda BudgetIT ta wallafa, wacce cibiya ce da ta shahara wajen bin diddigin manufofin kudi a Nijeriya.

Jihar ta zo matsayi na 6 daga cikin jihohi 36, inda ta samu maki 74 bisa 100.

  • Matafiya Sun Makale Sakamakon Ruftawar Gada A Hanyar Gombe Zuwa Bauchi

Rahoton ya yaba da irin nasarorin da Jihar Gombe ta samu a fannoni daban-daban da suka hada da nuna gaskiya a harkokin kasafi da kashe-kashen kudi, da nuna aminci da sahihanci a rahoton gudanar da kasafin kudi ta shafin yanar gizon jihar.

Wani babban abin lura ma shine tsarin kasafin kudin jihar na matsakaicin zango (MTEF), wanda aka bayyana shi a matsayin cikakke kuma mai kyakkywan tsari.

Rahoton ya tabbatar da cewa kasafin kudin Jihar Gombe da aka amince da shi ya cika sharuda da dama, yayin da harkokin kashe-kashen kudi na yanar gizon jihar ya kasance a saukake ga mai bukatar bincike da nazari.

Bugu da kari, Jihar Gombe ta kasance ta 7 a Nijeriya, yayin da a yankin Arewa maso gabas kuwa ta yi fintinkau a fannin gudanar da ayyuka cikin gaskiya da rikon amana, matsayin da ta samu daga cibiyar kula da harkokin kudi ta ƙasa (CETIW).

Farfesa kuma mai bincike da nazari a fannoni daban-daban, wanda kuma shi ne babban daraktan bincike da tattara bayanai a gidan gwamnati, Dr. Mu’azu Shehu ya bayyana cewa, bisa la’akari da yadda yake sanya ido sosai kan ayyukan gwamnati da kuma kimanta ci gaban kasa, Jihar Gombe ta yi fintinkau a fannin tafiyar da harkokin kudi cikin gaskiya da adalci da ɗorewar ayyuka na gari.

Ya yi nuni da cewa, shugabancin Gwamna Inuwa Yahaya ya taka muhimmiyar rawa wajen samar da shugabanci nagari da kuma tabbatar da gaskiya, tare da sanya Jihar Gombe a matsayin Jihar da samu shugabacin mai cike da riƙon amana ba tare da nuna wariya ba.

“Gwamnatin Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya tana ci gaba da jaddada kudirinta na tabbatar da gaskiya da rikon amana a kasafin kudi, wanda hakan ya sa Jihar Gombe ta samu karramawa a matakin kasa da na kasa da kasa. Musamman ma, a kwanan nan jihar ta samu lambar yabo na Bankin Duniya a Fannin tabbatar da gaskiya, adalci da dorewarsu wato (SFTAS) a fannoni dandan daban, hakan wata shaida ce dake nuna irin jajircewar gwamnatin Inuwa wajen kulawa da dukiyar talakawa.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Next Post
An Fara Zirga-Zirgar Motoci A Kan Babbar Gadar Cocody Da Kamfanin CRBC Na Kasar Sin Ya Gina A Kasar Kwadibwa

An Fara Zirga-Zirgar Motoci A Kan Babbar Gadar Cocody Da Kamfanin CRBC Na Kasar Sin Ya Gina A Kasar Kwadibwa

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version