CRI Hausa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home DAGA BIRNIN SIN

Gudummuwar Rigakafin COVID-19 Da Sin Ta Bayar Ya Isa Equatorial Guinea

by CRI Hausa
February 11, 2021
in DAGA BIRNIN SIN
1 min read
Gudummuwar Rigakafin COVID-19 Da Sin Ta Bayar Ya Isa Equatorial Guinea
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Wani bangare na allurar rigakafin COVID-19 na kamfanin Sinopharm da Sin ta bayar da gudummuwarta ga kasar Equatorial Guinea, ya isa Malabo, babban birnin kasar a jiya Laraba.

Yayin wani taron manema labarai a jiya, kakakin ma’aikatar harkokin wajen Sin, Wang Wenbin, ya ce wannan shi ne kashin farko na tallafin alluran rigakafi da gwamnatin Sin ta samar ga kasashen Afrika.
Da yake karbar rigakafin a filin jirgin saman Malabo, mataimakin shugaban kasar Teodoro Nguema Obiang Mangue, ya ce tallafin alama ce ta kyakkyawar dangantakar dake tsakanin kasashen biyu.
A nata bangaren, jakadiyar Sin a Equatorial Guinea, Qi Mei, ta ce yayin taron Sin da Afrika kan hadin gwiwar yaki da COVID-19 da ya gudana a watan Yunin 2020, Sin ta ba kasashen Afrika tabbacin kasancewa na farko da za su ci gajiyar alluran rigakafin kasar, kuma a yanzu, Sin din ta cika alkawarinta na bayar da rigakafin ga Equatorial Guinea, wanda zai taimaka mata cin galaba a kan cutar.
Ta kara da cewa, kasashen duniya sun yarda da nagarta da amincin alluran rigakafin na Sin. Ta ce duk da dimbin bukatar allurar da ake da ita a cikin kasar, Sin ta kuduri niyyar shawo kan kalubalen samar da ita kan farashi mai rahusa ga kasashe masu tasowa. (Mai fassarawa: Fa’iza Mustapha daga CRI Hausa)

SendShareTweetShare
Previous Post

CMG Ya Nuna Wani Shiri Dake Kara Bayyana Al’Adun Sinawa

Next Post

NIS Ta Bude Asibitin Jami’anta A Kan Iyakar Kasa Na Gurin

RelatedPosts

Sabon Nau’in Rigakafin Cutar COVID-19 Da Sin Ta Samar Zai Taimaka Wajen Yakar Cutar

Sabon Nau’in Rigakafin Cutar COVID-19 Da Sin Ta Samar Zai Taimaka Wajen Yakar Cutar

by CRI Hausa
16 hours ago
0

Daga CRI Hausa Shugaban cibiyar kandagarki da shawo kan cututtuka...

Yadda Shugaba Xi Jinping Yake Ba Da Jagoranci Ga Aikin Kula Da Lardin Qinghai

Yadda Shugaba Xi Jinping Yake Ba Da Jagoranci Ga Aikin Kula Da Lardin Qinghai

by CRI Hausa
16 hours ago
0

Daga CRI Hausa A jiya Lahadi, shugaba Xi Jinping na...

Shaidu Sun Karyata Jita-Jitar Da Ake Yadawa Game Da Alluran Riga-Kafin Cutar COVID-19 Na Kasar Sin

Shaidu Sun Karyata Jita-Jitar Da Ake Yadawa Game Da Alluran Riga-Kafin Cutar COVID-19 Na Kasar Sin

by CRI Hausa
16 hours ago
0

Daga CRI Hausa Jiya Lahadi, mamban majalisar gudanarwa kana ministan...

Next Post
NIS Ta Bude Asibitin Jami’anta A Kan Iyakar Kasa Na Gurin

NIS Ta Bude Asibitin Jami’anta A Kan Iyakar Kasa Na Gurin

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version