Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da Afirka Ta Kudu
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Za Ta Fafata Da Afirka Ta Kudu

byAbba Ibrahim Wada
2 years ago
Kofin duniya

Tawagar Super Eagles ta Nijeriya za ta fafata da Afirka ta Kudu da Benin da Rwanda da Zimbabwe da kuma Lesotho a wasannin rukuni na uku na gasar cin kofin duniya da za’a yi a shekara ta 2026.

A ranar Alhamis ne aka gudanar da bikin fitar da jadawalin wasannin a birnin Abidjan na kasar Ibory Coast wadda ita ce za ta karbi bakuncin gasar cin kofin nahiyar Afirka a shekara mai zuwa.

  • Matan Nijeriya Sun Buga Canjaras Da Kasar Canada A Wasan Farko Na Gasar Cin Kofin Duniya
  1. Sau 14 dai kasashen Nijeriya da Afirka ta Kudu suka fafata tsakanin su, inda Super Eagles ta yi nasara sau bakwai sannan suka yi canjaras biyu kuma karo na karshe da Nijeriya ta kara da Afirka Ta Kudun a wasan neman tikitin shiga gasar cin kofin duniya shi ne kafin gasar 2010.

Super Eagles ta samu nasara a wasanni biyu da suka fafata, amma Afirka ta Kudu ta samu gurbin shiga gasar la’akari da matsayin mai masaukin baki kamar yadda hukumar kwallon kafa ta duniya ta tsara.

Kasar Senegal, zakarun Afirka, na rukunin na biyu ne tare da Jamhuriyar Dimokaradiyyar Kongo da Togo da Mauritania da Sudan da kuma Sudan ta Kudu.

Sai Kasar Morroco, wadda ta kai wasan dab da karshe a gasar kofin duniya da aka buga a Katar – ta samu kanta a rukuni na biyar inda za ta kara da Zambia da Tanzania da Congo Brazzabille da Jamhuriyar Nijar da kuma Eritrea.

Ghana tana rukuni na daya tare da Mali, da Madagascar da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya, da Comoros da kuma Chadi kuma nan gaba kadan za’a saka ranar fara wasannin.

Cikakken Rukunin:
Rukuni na A: Masar, Burkina Faso, Guinea-Bissau, Saliyo, Ethiopia, da kuma Djibouti.
Rukuni na B: Senegal, Democratic Republic of Congo, Togo, Mauritania, Sudan da kuma Southern Sudan.
Rukuni na C: Nijeriya, Afirka ta Kudu, Benin Republic, Zimbabwe, Rwanda da kuma Lesotho.
Rukuni na D: Kamaru, Cape Berde, Angola, Libya, Eswatini da kuma Mauritius
Rukuni na E: Morroco, Zambia, Tanzania, Congo Brazzabille, Nijar da Eritrea.
Rukuni na F: Ibory Coast, Gabon, Kenya, Gambia, Burundi, da kuma Seychelles
Rukuni na G: Algeria, Guinea, Uganda, Mozambikue, Botswana, Somalia
Rukuni na H: Tunisia, Ekuatorial Guinea, Namibia, Malawi, Liberia, Sao Tome e Principe.
Rukuni na I: Ghana, Mali, Madagascar, the Central African Republic, Comoros da Chad. Za’a fara buga wasannin daga ranar 3 ga watan Nuwamban wannan shekarar
ta 2023, zuwa ranar 18 ga watan Nuwamban 2025 kuma kasashen Afirka na da gurbi tara, bayan da aka kara adadin kasashen da za su shiga gasar da za’a buga a shekarar 2026 zuwa 48.

Za dai a buga gasar a kasashen Amurka da Medico da kuma Canada daga ranar 11 ga watan Yuni zuwa 19 ga watan Yulin 2026, kasar Argentina ce dai ke rike da kofin gasar da ta dauka a shekarar 2022 da aka buga a Katar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane
Wasanni

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

October 7, 2025
Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni
Wasanni

Yanzu-Yanzu: Kwara United Ta Sallami Kocinta, Tunde Sanni

October 6, 2025
Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar
Wasanni

Kwallon Hockey: Nijeriya Na Fatan Samun Nasara A Masar

October 6, 2025
Next Post
An Bude Dandalin CMG Karo Na 2 A Shanghai

An Bude Dandalin CMG Karo Na 2 A Shanghai

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version