Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home KASUWANCI

Gwamanatin Akwa Ibom Ta Samu Yabo Kan Hadin Gwiwa Da Bankin Duniya

by Tayo Adelaja
September 25, 2017
in KASUWANCI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abubakar Abba

Kwamishinan Kudi na Jihar Akwa Ibom Nsikan Nkan ya yabawa Gwamnan Jihar Ibom Udom Emmanuel, saboda yin hadin gwiwa da Bankin Duniya don samar da ayyyukan da za su gina al’ummar jihar.

samndaads

Nsikan ya yi yabon ne lokacin da wata tawaga daga Bankin na Duniya suka ziyarci jihar don duba wa da kaddamar da  aikin Cibiyar kiwon lafiya da ke garin  Ikot Akpa Edung, cikin karamar hukumar Ibesikpo Asutan.

Kwamishinan ya bayyana cewar, dakin shan maganin wanda shi ne na farko a yankin zai taimaka wajen rage kalubalen harkar lafiya da al’ummar yankin ke fuskanta.

Ya danganta kawo aikin da Bankin Duniya ya yi yankin a bisa ayyukan inganta taruyuwar al’umma da gwamnan ya kirkiro da su a jihar, inda kuma ya yi kira ga daukacin al’ummar jihar da kada su gajiya wajen bai wa gwamnatin jihar goyon bayan su har zuwa bayan  da shekarar 2019.

Kwamishinan ya bayyana cewa, jihar cibiya ce ta zuba jari, inda ya roki tawagar ta Bankin Duniya da su yi amfani da damar wajen zuba jarinsu a jihar.

A nasa jawabin shugaban rikon kwarya na karamar hukumar, Barista Ukana Udofia ya gode wa Bankin na Duniya a bisa tagomashin da suka kawo yankin, inda ya tabbatar masu cewar za a yi amfani da dakin na shan magani kamar yadda ya dace.

Shi ma a nasa bayanin, shugaban kungiyar yankin, Dakta Sebastian Ibanga ya jinjina wa Bankin na Duniya aka ci gaban da suka kawo yankin, inda ya ce, dakin asibitin zai taimaka wa al’umar yanki matuka a kan harkar lafiyarsu.

Ya yi nuni da cewa, saboda rashin asibiti a yankin, yana haifar da rasa ran mata masu juna biyu a yankin, ya kuma yi roko ga tawagar na Bankin Duniya da kada su gajiya wajen kara samar da wasu asibitocin ga sauran kauyukan da ke jihar.

SendShareTweetShare
Previous Post

An Karrama Shugaban Bankin Zenith Da Lambar Yabo A Amurka

Next Post

Tsakanin Al-Makura Da Ma’aikatan Gwamnati

RelatedPosts

Sugar

Alakar Dake Tsakanin Sukari Ca Ciwon Suga

by Muhammad
2 weeks ago
0

Da yawa a yankin kasashen nahiyar Afirka ana ganin sukari...

A Na Cigaba Da Zaman Doya Da Man Ja Tsakanin Majalisa Da Shugaba Trump

Ba Da Mugun Nufi Shugaba Buhari Ya Garkame Iyakoki Ba – Ministar Kudi

by Abdulaziz Kabir Muhammad
1 year ago
0

Ministar kudi da tsaretsare, Uwargida Zainab Ahmed Shamsuna, ta sanar...

Gwamnatin Tarraya Ta Kebe Biliyan N2.6 Don Aikin Tashar Mambilla A 2020

by Abdulaziz Kabir Muhammad
1 year ago
0

Sama da shekaru arba’in da suka shude kenan da bada...

Next Post

Tsakanin Al-Makura Da Ma’aikatan Gwamnati

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version