Umar Faruk">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Gwamna Bagudu Ya Jinjina Wa Buhari Kan Nadin Yelwa Shugaban HYPPADEC 

by Umar Faruk
February 2, 2021
in LABARAI
2 min read
Gwamna Bagudu Ya Jinjina Wa Buhari Kan Nadin Yelwa Shugaban HYPPADEC 
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Gwaman jihar kebbi, Sanata Abubakar Atiku Bagudu ya yaba da yadda shugaban kasa Muhammadu Buhari ya nada dan asalin jihar Kebbi, Alhaji Abubakar Sadik Yelwa a matsayin babban manajan darakta na hukumar bunkasa yankunan samar da wutar lantarki (HYPPADEC).

Sanata Abubakar Atiku Bagudu, Gwamnan Jihar Kebbi ne ya yi wannan yabo a yayin gudanar da bikin liyafar bankwana da aka shirya a jiya ga Sadik Yelwa a fadar Gwamnatin jihar ta Kebbi da ke Birnin Kebbi.
Bagudu ya ce” Shugaba Muhammadu Buhari nadin Sadik Yelwa wani namiji kokarin wurin zakulu Abubakar Sadik Yelwa don nadinsa sabon manajan darakta na sabuwar hukumar da aka kafa don bunkasa yankunan samar da wutar lantarki wato (HYPPADEC) na farko a hukumar, yana mai shawartar wanda aka nada ya tabbatar da ya yi aiki tukuru don sauke nauyin da aka dora masa na zama shugaban hukumar.
Gwamnan ya kuma nuna farin cikisa da yabawa ga Shugaba Muhammadu Buhari kan nada wasu ‘yan asalin jihar Kebbi da suka cancanta a cikin manyan mukamai a matakin Gwamnatin Tarayya.
Bagudu ya ci gaba da ambato wadanda shugaban kasa ya baiwa mukamai daga jihar ta kebbi, kamar Alhaji Atiku Bunu matsayina Kwamishinan a Hukumar tabbatar da bin tsarin daukar ayyukkan gwamnatin Tarayya wato (federal character commission), Alhaji Ahmad Sama, Kwamishinan a Hukumar Kula da Ma’aikata da tsarin gudanar da aikin gwamnatin Tarayya wato federal cibil serbice commission , Alhaji Hussaini Kangiwa a matsayin Shugaban Hukumar Kula da Nakasassu, Hassan Bello a matsayin shugaban hukumar kula da sufurin ta Jirgin Ruwa wato (Nijeriya shippers council), sai kuma Hassan Koko na Hukumar Tashar Jiragen Ruwa wato (Nijeriya Port Authority).
Sauran sun hada da Darakta janar a hukumar dauka da samar da ayyukkan yi ta kasa wato (National Directorate of Employment), Dakta Nasir Ladan Argungu yayin da yake fatan cewa majalisar dattijai za ta amince da nadin Farfesa Audu .A Zuru a matsayin kwamishina na Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta kasa (INEC) wanda zai wakiltar jahohin Arewa maso Yamman kasar nan.
Gwamnan dai ya bayyana kwamishinan filaye da gidaje Abubakar Sadik Yelwa irin ci gaban da ya samar a ma’aikar filaye da gidaje ta jihar Kebbi kafin barin gado, ya kara da cewa Alhaji Sadik Yelwa a mutum mai matukar girmamawa wanda ya ba da gudummawa ga ci gaban Jihar ta Kebbi a dukkan bangarori na aikin gwamnatin jihar bakidaya.
Bugu da kari ya ce Yelwa a lokacin mulkinsa a matsayin Kwamishinan filaye da gidaje ya bullo da ayyukan gine-gine da kuma tsarin rabon filaye ga al’ummar jihar guda dubu 22 wanda ya kamata a aiwatar tare da bullo da wani tsarin da ake Kira AGIS a Ma’aikatar filaye da gidaje yayin zaman shi Kwamishinan.
Da yake mayar da martani, sabon Manajan Daraktan na HYPPADEC, Alhaji Abubakar Sadik Yelwa ya gode wa gwamnan kan wannan dama da ya ba shi na yin aiki a cikin majalisar zartarwa ta jihar Kebbi, inda ya bayyana Gwamna Abubakar Atiku Bagudu a matsayin kwarzon jagoranci wanda ya baiwa Kwamishinan da sauran mukaraban sa damar gudanar da ayyukka a ma’aikatun su ba tare da wata matsala ba. Ya ci gaba da cewa gwamna Atiku Bagudu ya taimakawa rayuwarsa tun lokacin da yana karatu a jami’a har zuwa yau. Saboda haka ina godiya kwarai da gaske.
Daga karshe Sadik Yelwa ya kuma godewa gwamnan bisa ga irin goyon bayan da yake baiwa ma’aikatar filaye. Ya yi baiwa gwamnan tabbacin cewa Hukumar za tayi hada gwiwa da Gwamnatin Jihar Kebbi wajen aiwatar da shirye-shiryenta kan ayyukkan da zata gudanar.

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Ku Kyautata Alaka Da Jama’a A Yakin Tsaro – Zulum Ga Shugabanin Sojoji

Next Post

Gwamna Ganduje Ya Kaddamar Da Dakarun Yaki Da Korona 2,000 A Kano

RelatedPosts

Harin Boko Haram: Gwamnatin Borno Ta Tabbatar Da Mutuwar Mutum 10

Harin Boko Haram: Gwamnatin Borno Ta Tabbatar Da Mutuwar Mutum 10

by Umar Faruk
1 hour ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim Gwamnan Borno, Farfesa Babagana Umara Zulum ya...

Saura Wata Biyu Buhari Ya Dawo Da Zaman Lafiya –Sanata Lawan

by Umar Faruk
6 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya, Shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata Ahmad...

Sojoji Sun Sake Kwato Garin Marte A Borno

Sojoji Sun Sake Kwato Garin Marte A Borno

by Umar Faruk
15 hours ago
0

Daga Sulaiman Ibrahim Sojojin Nijeriya a yammacin yau, da misalin...

Next Post
Gwamna Ganduje Ya Kaddamar Da Dakarun Yaki Da Korona 2,000 A Kano

Gwamna Ganduje Ya Kaddamar Da Dakarun Yaki Da Korona 2,000 A Kano

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version