Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Shago 6000 A Kasuwar Buni-Yadi

by
6 months ago
in LABARAI
2 min read
Gwamna Buni
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Muhammad Maitela Damaturu,

 

Gwamnan Jihar Yobe, Hon. Mai Mala Buni, ya kaddamar da sabbin shaguna 6000 wadanda gwamnatin jihar tare da hadin gwiwa da hukumar UNDP ta Majalisar Dinkin Duniya suka gina a kasuwar Buni-Yadi, a karamar hukumar Gujba da ke jihar.

Labarai Masu Nasaba

“Ina Cikin Wani Hali, An Kashe Matata Da Ciki Wata 9 Da Yara 4” —Mijin Matar Da IPOB Suka Kashe

An Karrama Buhari Da Lambar Yabo Kan Kwazonsa Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

 

Gwamna Buni shi ne ya bayyana hakan a jawabinsa ga dubban jama’ar da suka halarci bikin bude sabbin shagunan, ranar Litinin a Buni- Yadi.

 

Har ila yau, ya kara da cewa aikin gina kasuwar ya zo ne a karkashin ayyukan sake farfado da yankunan da matsalar tsaron Boko Haram ta shafa don sake inganta walwala da ci gaban jama’a bayan lafawar rikicin.

 

A hannu daya kuma, Gwamna Buni ya yi karin haske dangane da yadda aikin sake gina kasuwar zai farfado da harkokin kasuwancin da aka san garin da shi, wanda ya kasance hadakar ‘yan kasuwa daga jihohin Borno, Taraba, Adamawa da Kano.

 

ADVERTISEMENT

“Wannan aikin zai farfado da ci gaban tattalin arziki a wannan yanki tare da bunkasa kudin shiga ga jama’a domin dawo da walwala, inganta yanayin rayuwa kamar yadda wannan gwamnatin ta kuduri aniya.” in ji shi.

 

Haka kuma Gwamna Buni ya umurci shugaban karamar hukumar ta dauki ingantattun matakai wajen ganin an bi hanyar da ta dace na raba shagunan ga wadanda suka cancanta.

 

Bugu da kari kuma, a Buni- Gari, Gwamna ya kaddamar da bude makarantar firamari (International Primary School) wadda kamfanin Shell Petroleum Debelopment Company (SPDC), hadi da gwamnatin jihar suka gina.

 

Yayin da ya bayyana cewa gwamnatinsa a shirye take wajen aiki kafada da kafada da sauran kungiyoyin tallafi don samun ci gaban jihar.

 

Sa’ilin da yake yaba wa hukumar SPDC dangane da wannan hubbasa, Gwamna Buni bukaci karamar hukumar ta samar da cikakken tsaro a makarantar.

 

Da yake tofa albarkacin bakinsa, Kwamishina Ma’aikatar Kula da Ayyukan Jinkai da Abubuwan da Suka Shafi Ibtila’i a jihar, Dakta Abubakar Iliya, ya ce makarantar ta kunshi rukunan ajujuwa (blocks) hudu da ajujuwa 16.

 

Ya kara da cewa baya ga wannan, akwai sashen gudanarwa, dakin gwaje-gwajen kimiyya, sashen fasahar sadarwa (ICT) tare da wutar lantarki mai amfani da hasken rana da rijiyar burtsatse da makamantan su.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Labarin Yarinyar Da Mijinta, Wanta, Wan Mijinta, Da Mijin Yayarta Suka Yi Mata Ciki: Jaraba Ko Alkaba’i?

Next Post

Me Ya Sa Kungiyar Farfado Da Martabar Arewa Ta Ki Gayyato Jaridun Hausa Wajen Taronta?

Labarai Masu Nasaba

“Ina Cikin Wani Hali, An Kashe Matata Da Ciki Wata 9 Da Yara 4” —Mijin Matar Da IPOB Suka Kashe

“Ina Cikin Wani Hali, An Kashe Matata Da Ciki Wata 9 Da Yara 4” —Mijin Matar Da IPOB Suka Kashe

by Leadership Hausa
4 hours ago
0

...

An Karrama Buhari Da Lambar Yabo Kan Kwazonsa Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

An Karrama Buhari Da Lambar Yabo Kan Kwazonsa Wajen Yaki Da Cin Hanci Da Rashawa

by Muhammad Bashir
6 hours ago
0

...

IPOB Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Wata Mata Bahaushiya Da Yaranta 4 A Anambra

IPOB Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Wata Mata Bahaushiya Da Yaranta 4 A Anambra

by Muhammad Bashir
15 hours ago
0

...

Nijeriya Zata Ringa Kashe Miliyan 999 Kullum Wurin Ciyar Da ‘Yan Firamare Miliyan 10

Nijeriya Zata Ringa Kashe Miliyan 999 Kullum Wurin Ciyar Da ‘Yan Firamare Miliyan 10

by
16 hours ago
0

...

Next Post
Arewa

Me Ya Sa Kungiyar Farfado Da Martabar Arewa Ta Ki Gayyato Jaridun Hausa Wajen Taronta?

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: