Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Wa Matar Da 'Yan Bindiga Suka Raba Da Muhallinta Shatara Ta Arziki
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Wa Matar Da ‘Yan Bindiga Suka Raba Da Muhallinta Shatara Ta Arziki

byLeadership Hausa
2 years ago
gwamna

A jiya Alhamis ne Gwamna Dauda Lawal na Jihar Zamfara ya karɓi baƙuncin matar nan da ‘yan bindiga suka raba da muhallinta da aka yaɗa a wani faifan bidiyo.
Faiaifan bidiyon ya nuna wata uwa da ‘ya’yanta tana bayani a kan ‘yan bindiga suka tilasta musu cin ciyawa domin su tsira da rayukansu.
Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar ta Zamfara, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, ta ce halin da matar wacce ta rasa matsugunin ke ciki ya nuna cewa akwai bukatar a ɗauki matakin gaggawa don magance musabbabin Ibtila’in da yake raba mutane da muhallansu same su da kuma samar matakawuna da kuma tabbatar da cewa iyalai suna samun abubuwan bukata na rayuwa.

  • Tirka-tirkan Takardun Tinubu: Ku Zo Mu Hada Hannu Don Fafutukar Wanzar Da Gaskiya – Atiku Ya Roki Obi, Kwankwaso
  • NIS Ta Samar Da Fasfo 204,332 Cikin Mako Uku – Adepoju

Ta ƙara da cewa Gwamnan ya karɓi baƙuncin matar da ta rasa muhallin nata ne a matsayin nuni kan jajircewarsa wajen kare rayuka da dukiyoyin al’ummar Zamfara.

gwamna
“A yau (Alhamis) ne Gwamna Dauda Lawal ya karbi baƙuncin Hauwa’u Halliru, wadda ta rasa komi a dalilin tu’annatin ‘yan fashin daji.
“Gwamna Lawal ya bayyana ƙudirinsa na kawo ƙarshen rashin tsaro a jihar tare da jajanta wa iyalan da ɓarnar ‘yan fashin dajin ta shafa.
“A matsayinsa na shugaba mai tausayi, Gwamna Lawal ya gaggauta samar wa matar da ta rasa muhallin nata gida mai kyau da aka sa wa komai na more rayuwa.
“Ya kuma tabbatar mata da kudirin gwamnatinsa na ciyar da iyalinta abinci da sauran abubuwan bukatu, ta yadda za ta sake gina rayuwarta cikin mutunci da tsaro.
“Bugu da kari, gwamnan ya umarci kwamishinan ilimi, kimiya da fasaha da ya tabbatar da shigar da ‘ya’yanta makaranta cikin gaggawa da kuma samun cikakken tallafin karatu.

“Ya kuma bukaci dukkan hukumomin da abin ya shafa da su ƙara ƙaimi wajen zakulo iyalai marasa galihu da ke fuskantar irin wannan ƙalubale tare da ba su tallafin da ya dace.
“A nasa jawabin, Shugaban Ƙungiyar Masu Kare Hakkin Bil’adama, Kwamared Salisu Umar, ya bayyana matukar jin daɗinsa kan yadda Gwamnan Jihar Zamfara ke ƙoƙarin tabbatar da tsaro da jin daɗin jama’a.
“Ya kuma yaba da yadda gwamnan ya nuna himma, tare da bayyana cewa wannan ne karon farko da ya ga irin wannan kyakkyawar shugabanci a jihar, inda ya ƙara da cewa kalaman nasa sun yi daidai da ra’ayoyin jama’a, wadanda suka dade suna jiran shugaban da zai riƙa sanya buƙatunsu a gaba.” In ji sanarwar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci
Labarai

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Next Post
Shawarar Kasar Sin Ta Gina Al’ummar Duniya Mai Mokamar Bai Daya

Shawarar Kasar Sin Ta Gina Al’ummar Duniya Mai Mokamar Bai Daya

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version