Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Inuwa Ya Gabatar Wa Shugaban Kasa Taswirar Gina Masana’antu

by
8 months ago
in LABARAI
2 min read
Gwamna Inuwa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Khalid Idris Doya, Gombe

 

Gwamnan Jihar Gombe Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, ya gabatar wa shugaban kasa Muhammadu Buhari taswirar tsarin kafar cibiyar masana’antu da aka mata lakabi da ta ‘Muhammadu Buhari’ da gwamnatin jihar ta bada kwangilarsa.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Ganduje Ta Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 A Kano

‘Yan Arewa Masu Kai Abinci Yankin Inyamurai Su Dakatar Saboda Kisa –Matasan Arewa A Kudu

 

Wannan matakin na zuwa ne a yayin wata ziyarar baya-bayan nan da gwamnan ya kai wa shugaba Buhari a fadarsa da ke Abuja, inda kuma suka tattauna kan muhimman batutuwa da suka shafi jihar da ma kasa baki daya.

 

A wata sanarwar da Ismaila Uba, kakakin gwamnan Gombe ya fitar, ya nakalto cewa, shugaban ya yi alkawarin bada goyon bayan gwamnatin tarayya ga kokarin gwamnan na tabbatar da tsaro da zaman lafiya dama bunkasa ci gaban tattalin arziki da zamantakewa.

 

Daga bisani gwamnan ya shaida wa manema labarai na fadar shugaban kasan cewa, idan aka kammala aikin cibiyar, ba kawai tattalin arzikin jihar za ta bunkasa ba har ma da samar da ayyukan yi ga dimbin matasa a ciki da wajen jihar.

 

Ya ce, “Mun tattauna kan batun cibiyar masana’antu wacce muka bada kwangilar gina ta da aka sanya sunan mai girmama shugaban kasa ‘Muhammadu Buhari’, na shaida masa haka kuma na nemi taimakonsa don ganin hakar mu ta cimma ruwa.”

 

“Mafiya yawan al’ummarmu kananan manoma da makiyaya ne, idan muka yi nasarar kafa wannar cibiya, zamu samar da manyan damammaki ga matasanmu a harkokin masana’antu da noma da sarrafa kayayyakin noman da kasuwancinsu dama rarraba su don su samu kyawawan hanyoyin dogaro da kai da habaka tattalin arziki.”

 

Gwamna Inuwa Yahaya ya ce, sun kuma tattauna kan matsalar tsaro, duba da cewa Jihar Gombe tana taka muhimmiyar rawa wajen karban bakuncin ‘yan gudun hijira daga jihohin Borno da Yobe da Adamawa wadanda rikicin Boko Haram ya shafa, lamarin da ke haifar da tsaiko ga ababen more rayuwa.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Tabargazar Garkuwa Da Dalibai A Nijeriya

Next Post

Abin Da Ya Sa Na Karbi Khalifancin Darikar Tijjaniyya – Sanusi Lamido Sanusi 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Ganduje Ta Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 A Kano

Gwamnatin Ganduje Ta Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 A Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
13 mins ago
0

...

‘Yan Arewa Masu Kai Abinci Yankin Inyamurai Su Dakatar Saboda Kisa –Matasan Arewa A Kudu

‘Yan Arewa Masu Kai Abinci Yankin Inyamurai Su Dakatar Saboda Kisa –Matasan Arewa A Kudu

by
6 hours ago
0

...

EFCC Ta Bankado Gidaje 17 A Nijeriya Da Kasashen Waje Na Akanta Janar

EFCC Ta Bankado Gidaje 17 A Nijeriya Da Kasashen Waje Na Akanta Janar

by
18 hours ago
0

...

Ana Kokarin Siffanta Kungiyar Dattawan Arewa A Matsayin Mai Zuga ‘Yan Tawaye A Nijeriya – Dr. Hakeem

Ana Kokarin Siffanta Kungiyar Dattawan Arewa A Matsayin Mai Zuga ‘Yan Tawaye A Nijeriya – Dr. Hakeem

by Abdulrazaq Yahuza Jere
1 day ago
0

...

Next Post
Sanusi Lamido Sanusi 

Abin Da Ya Sa Na Karbi Khalifancin Darikar Tijjaniyya - Sanusi Lamido Sanusi 

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: