Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudurinsa Na Bai Wa Ɓangaren Shari'a 'Yanci Don Samar Da Adalci A Zamfara
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudurinsa Na Bai Wa Ɓangaren Shari’a ‘Yanci Don Samar Da Adalci A Zamfara

bySulaiman
10 months ago
Lawal

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya bayyana cewa gwamnatinsa ta duƙufa wajen ba da fifiko ga tsare-tsare da ke inganta tabbatar da adalci a kan lokaci da kuma kare ’yancin ɓangaren shari’a.

 

Gwamnan ya bayyana haka ne a ranar Litinin ɗin da ta gabata a wajen taron ƙara wa juna sani ga alƙalai da ma’aikatan kotuna a babbar kotun shari’a ta Jihar Zamfara, wanda aka gudanar a harabar babbar kotun da ke Gusau.

  • Babbar Kasa Mai Farar Aniya: Shin Har Yanzu Akwai Masu Son Lalata Dangantakar Sin Da Afrika?
  • Nakasa A Mahangar Karin Magana: Guzurin Ranar Nakasassu Ta Duniya

A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar, taron ya samar da wata dama ga jami’an shari’a da masu ruwa da tsaki domin tantance ayyukan da bangaren shari’a ke yi, da gano ƙalubale, da kuma kafa sabbin manufofi.

 

A jawabinsa na bufe taron, Gwamna Lawal ya amince da jajircewa da jagoranci na ƙwarai na Babbar Alƙalin Alƙalan Jihar, Mai Shari’a Kulu Aliyu, OFR, FNJI, da ɗaukacin bangaren shari’a bisa jajircewarsu na sauke nauyin da aka ɗora musu.

 

Ya ce, “jajircewarta wajen tabbatar da adalci yana ƙara ƙwarin gwiwa da kuma ƙara wa bangaren shari’a aminci a matsayin wata cibiya mai muhimmanci a tsarin dimokuraɗiyya. Wannan gwamnati ta tsayu tsayin daka wajen tallafa wa bangaren shari’a a dukkan ayyukanta.

 

“Gwamnatina za ta ci gaba da ba da fifiko ga shirye-shiryen da za su inganta samar da adalci a kan lokaci da kuma kare ‘yancin wannan bangare na gwamnati.”

 

Gwamna Lawal ya bayyana cewa, taron ƙara wa juna sanin na da matuƙar muhimmanci. “Zai inganta fasaha da kuma ilimantar da mahalarta domin su kasance cikin shiri sosai don yin hidima da biyan buƙatun jama’a. Jama’ar mu na kallon ku a matsayin matita ga talakan ƙasa wajen ganin ya samu adalci tare da kare haƙƙinsa. Dole ne jami’an shari’a da ma’aikatan su kasance cikin shiri sosai don cimma waɗannan manufofi, musamman a waɗannan lokutan da ake fuskantar ƙalubale.

 

“Babbar Alƙalin Alƙalai, alƙalan babbar kotun jihar Zamfara, manyan mahalarta taron, abin farin ciki ne ganin irin matakan da hukumar shari’a ke ɗauka wajen tsare-tsaren ma’aikatan Majistare da sauran ma’aikatan shari’q domin tabbatar da adalci.

 

Gwamnan ya kuma buƙaci bangaren shari’a da su yi taka-tsan-tsan a kan wasu ’yan tsirarun da ɗabi’unsu za su iya gurgunta mutuncin wannan hukuma. “Ganowa tare da magance rashin ɗa’a a bangaren wani nauyi ne da ke buƙatar himma, mutunci, da sadaukarwa.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya
Labarai

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba
Labarai

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci
Labarai

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Next Post
Sin Ta Yi Maraba Da Amincewar Da UNGA Ya Yi Da Kudurin Wanzar Da Zaman Lafiya Da Kasar Ta Gabatar

Sin Ta Yi Maraba Da Amincewar Da UNGA Ya Yi Da Kudurin Wanzar Da Zaman Lafiya Da Kasar Ta Gabatar

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version