Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RAHOTANNI

Gwamna Masari Yayi Kira Ga Masu Cutar Kanjamau

by Tayo Adelaja
September 13, 2017
in RAHOTANNI
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga El-Zaharadeen Umar, Katsina.

Gwamnan jihar Katsina Alhaji Aminu Bello Masari ya ja hankali masu dauke da cuta mai karya garkuwar jiki (wato SIDA) da su zama masu amana da gaskiya a yanayin mu’amularsu  da zamantakewarsu cikin al’umma.

Alhaji Aminu Bello Masari ya yi wannan jan hankali ne lokacin da kungiyar masu dauke da cuta mai karya garkuwar jiki suka kai masa ziyara a fadar gidan gwamnatin jihar Katsina.

Ya kuma kara da cewa gwamnatinsa a shirye ta ke ta taimaka wajan ganin  an taimakawa mambobin wannan kungiyar wajan kula da da kuma bada magunguna da za su taimaka masu kwarai da gaske akan wannan lalura da suke dauke da ita.

Gwamna Aminu Bello Masari ya sha alwashi taimakawa kungiyar wajan ganin ta shirya zaban shuwagabaninta inda ya bada tabbacin mika rahotan abubuwan da suke bukata domin gwamnati ta gani ta kuma san abin yi.

Tunda farko da yake nasa jawabin shugaban kungiyar masu dauke da cuta mai karya garkuwar jiki  Malam Shehu Ibrahim ya ce sun zo gidan gwamnati ne domin kawo ziyarar girmamawa da kuma bayyana wasu daga cikin matsalolin da suke fuskanta.

Inda ya bayyana cewa suna da bukatar dauka mataki na so sai akan mambobin su dangane da magunguna da ake ba su, domin kare su daga fadawa cikin wani hali na daban.

Shugaban ya kuma nuna bukatar da kungiyar ke da ita da mota mai daukar mutun goma sha takwas wanda ya ce idan gwamnati ta ba kungiyar zata taimaka wajan cigaba da aikin kungiyar ke yi na fadakar da jama’a dangane da wannan lalura.

SendShareTweetShare
Previous Post

Tilasta Wa ’Yan Takara Ba Dimokuradiyya Ba Ne –Hon. Wadada

Next Post

Da Gaske Akwai Zinare A Kan Masu Sanko?

RelatedPosts

Babandede Ya Yi Gargadi A Kan Daukan Aiki Na Bogi Da Sunan NIS

Sauye-sauye Masu Ma’ana A Sashen Fasfo Na Hukumar Shige Da Ficen Nijeriya

by Yahuzajere
1 day ago
0

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya (NIS), karkashin...

An Gabatar Da Huduba Kan Ramadan A Babban Masallacin Jos

An Gabatar Da Huduba Kan Ramadan A Babban Masallacin Jos

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Daga Mohammed Ahmed Baba, Jos A ranar Juma'ar nan ne...

Yadda Tu’amalli Da Kayan Maye Ke Shafar Lafiyar Matasa Maza Da Mata  – Margaret

Yadda Tu’amalli Da Kayan Maye Ke Shafar Lafiyar Matasa Maza Da Mata  – Margaret

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Uwargida  Margaret  Juliu, sananniyar ce a jihar Kaduna,  musamman wajen fadakar...

Next Post

Da Gaske Akwai Zinare A Kan Masu Sanko?

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version