Gwamna Nasir Ya Gabatar Da Kasafin Kudin Naira Biliyan 250 Ga Majalisar Dokokin Kebbi
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Nasir Ya Gabatar Da Kasafin Kudin Naira Biliyan 250 Ga Majalisar Dokokin Kebbi

bySadiq
2 years ago
Nasir

Gwamna Nasir Idris na Jihar Kebbi, ya gabatar da kasafin kudi naira biliyan 250, 134, 091, 757.01 na shekarar 2024 na samar da ababen more rayuwa da kuma ayyukkan ciyar da al’ummar jihar a gaban majalisar dokoki don damar amincewa da kasafin kudin.

Dakta Nasir ya bayyana hakan ne a ranar Laraba a zauren majalisar da ke Birnin Kebbi.

  • Bunkasuwar Sin Na Taka Rawa Ga Farfadowar Yankin Asiya Da Pacific
  • BRICS Ta Bi Sahun Sassan Dake Neman Kawo Karshen Rikicin Isra’ila Da Palasdinu

Kasafin kudin samar da ababen more rayuwa da karfafa wa al’ummar jihar da kuma biyan bukatun ‘yan jihar da kuma cika alkawuran da aka dauka a yayin yakin neman zabe da aka yi wa jama’armu.

Gwamnan, ya ce a yayin gabatar da kasafin kudin na shekarar 2024 da za a kashe kudaden da ake kashewa akai-akai na biliyan 90.6, yayin da manyan kudaden da za a kashe ya kai biliyan 159.4.

Wasu muhimman sassa na tattalin arzikin jihar sun samu karin kasafin kudi saboda matakin da gwamnati ta dauka na samar da sabon shirin jihar Kebbi.

Ya ce wani bangare na shirin shi ne “magance batutuwan da suka hada da samar da ayyukan yi ga matasa da mata, gyara makarantu, gina hanyoyi, tsaro da samar da ingantaccen ruwan sha da kalubalen muhalli a jihar.

“A karkashin kasafin kudin 2024, nan take za mu kara habaka manufofinmu da aka tsara da kuma dorewar shirinmu a jihar”.

Dokta Nasir ya ce shirin gwamnatin na samar da ababen more rayuwa zai yi nisa wajen samar da hanyoyin samar da ababen more rayuwa da inganta rayuwar al’ummar jihar ta Kebbi kai tsaye, wanda hakan zai shafi al’ummar Jihar Kebbi kai tsaye, inda ya kara da cewa irin wannan shirin zai shafi gyaran makarantu da gina tituna da kuma zamanantar da jihar.

“Kudirin kasafin kudin shekarar 2024 na nuni da cewa an zuba jari mai yawa wajen samar da ingantaccen ruwan sha, da karfafawa mata da kungiyoyin matasa ta hanyar samar da ayyukkan yi.

Ya kuma ba da tabbacin ga ‘yan majalisar jihar na ci gaba da zaman lafiya da zamantakewar aiki.

Yayin da yake jinjina wa majalisar dokokin jihar kan kokarin da suke yi na nuna kyakykyawan sakamako doka ga daukacin al’ummar jihar.

A nasa martanin, kakakin majalisar dokokin jihar, Hon. Usman Muhammad ya bai wa gwamna Nasir Idris tabbacin yin gaggawar amincewa da kasafin kudin shekarar 2024 da aka gabatar wa majalisar domin amincewa.

Yayin da yake yi wa gwamnan alkawarin tabbataci da kasafin kudin da za a kashe zai biya bukatun ‘yan jihar domin ‘yan majalisar su ma wakilan jama’ar jihar ne daga mazabu daban-daban na jihar.

Daga karshe ya gode wa gwamna Nasir Idris bisa jajircewarsa ga ci gaban jihar da al’ummarta.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Lauyoyi Sun Bukaci Kotun ECOWAS Ta Haramta Takunkumi Kan Nijar

Lauyoyi Sun Bukaci Kotun ECOWAS Ta Haramta Takunkumi Kan Nijar

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version