Gwamna Sani Zai Kaddamar Da Cibiyar Kula Da Cutar Kansa Mai Gadaje 300 A Kaduna - Kwamishina
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Sani Zai Kaddamar Da Cibiyar Kula Da Cutar Kansa Mai Gadaje 300 A Kaduna – Kwamishina

bySulaiman
1 year ago
Sani

Gwamna Uba Sani ya yi alkawarin kammalawa tare da kaddamar da wani asibitin kwararru mai gadaje 300 wanda aka tanada musamman don kula da masu cutar kansa a Millennium city, da ke Kaduna a karshen shekarar 2024.

 

Wannan aikin asibitin wanda tsohon mataimakin shugaban kasa, Namadi Sambo ya kaddamar, ya samu tallafin dala miliyan 148 daga bankin cigaban Musulunci (IDB) da nufin samar da cikakkiyar cibiyar kiwon lafiya ga al’ummar jihar Kaduna.

  • Zaɓen Ƙananan Hukumomi: Gwamna Uba Sani Ya Ƙaddamar Da Yaƙin Neman Zaɓen APC
  • Sanatocin Arewa 12 Da Suka Gaza Gabatar Da Ƙudiri A Watanni 15

Duk da kokarin da gwamnatocin baya da suka hada da na Patrick Yakowa, Mukhtar Ramadan Yero, da Nasir Ahmed El-Rufai suka yi, har yanzu aikin bai kammala ba.

 

Da take magana, kwamishiniyar lafiya ta jihar Hajia Umma K. Ahmed a wani taron manema labarai a ranar Laraba, da take bayyana irin nasarorin da gwamnatin Sanata uba Sani ta samu a fannin kiwon lafiya, ta ce, Gwamna Sani ya ce: “A cikin zango na karshe na shekarar 2024, zai gayyace ‘yan jarida domin kaddamar da kammala ginin wannan katafariyar cibiyar kiwon lafiya ta zamani.

 

“Kaddamar da wannan cibiya ta zamani, za ta kawo sauyi tare da gyara harkokin kiwon lafiya na Jiha tare da rage yawan fita zuwa kasashen ketare don neman magani, domin asibitin mai gadaje 300 yana da sashen binciken cututtukan daji da kuma magance cutar. ”

 

Gwamnan ya ce, tsaren-tsaren inganta kiwon lafiya ya bada fifiko matuka wajen samar da kayan aiki a dukkan matakan kiwon lafiya da suka hada da na farko, matsakaita da manya a jihar, inda ya ce, gwamnati na inganta manyan asibitoci 9, inda aka zabo uku-uku daga cikin shiyyoyi Uku da ke jihar.

 

“Asibitocin sun hada da Asibitin Maigana, Asibitin Rigasa, Asibitin Gwantu, Asibitin Ikara, Asibitin Patrick Ibrahim Yakowa, da Asibitin Giwa.”

 

Sauran sun hada da “Sabon Asibitin Tunawa da Dabo Lere, Asibitin Sabon Tasha, da Asibitin Kachia”. in ji ta.

 

Wadannan Asibitocin, a halin yanzu suna cikin matakai daban-daban na sake ginawa, sake fasali, da kuma samar da kayan aiki a matsayin wani bangare na shirin Gwamnati na inganta cibiyoyin kiwon lafiya.

 

Gwamnan ya kara da cewa, ana kokarin samar da ababen more rayuwa ne domin ganin an samu sauyi a kowane mataki domin samar da ingantacciyar kulawa ga al’ummar jihar Kaduna.

 

Hajiya Umma ta jaddada cewa: “Tun da ya hau kan karagar mulki a ranar 29 ga Mayu, 2023, Gwamna Uba Sani ya nuna jajircewarsa na kawo sauyi a fannin kiwon lafiya.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Next Post
Sin Ta Bukaci Kwamitin Sulhun MDD Da Ya Ingiza Sassauta Rikicin Lebanon Da Isra’ila

Sin Ta Bukaci Kwamitin Sulhun MDD Da Ya Ingiza Sassauta Rikicin Lebanon Da Isra’ila

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version