Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Gwamna Zulum Ya Bude Cibiyoyin Kiwon Lafiya Biyar A Maiduguri 

by
1 year ago
in LABARAI
1 min read
Gwamna Zulum
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Muhammad Maitela,

Gwamnan jihar Borno, Prof. Babagana Umara Zulum ya bude cibiyoyin kiwon lafiya guda biyar a kwaryar birnin Maiduguri tare da kammala aikin gyaran babbar hanyar da ta tashi daga Maiduguri zuwa Bama, da sauran muhimman ayyuka, a ranar Laraba.

Karin ayyukan da Gwamnan ya bude sun hada da cibiyoyin kiwon lafiya matakin farko guda hudu da ke kan hanyar Baga, Njimtilo, rukunin gidaje 777 da a Abujan Talakawa, tare da asibitin cutuka masu saurin yaduwa da ke kan hanyar Kirikasamma.

Labarai Masu Nasaba

Tukunyar Gas Ce Ta Fashe Ba Bam Ba —Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

Bugu da kari, Zulum ya bude aikin hanyar unguwar Abuja-Sheraton wanda daga bisani kuma ya dora harsashen ginin gina sabuwar asibiti mai gadaje 50 a unguwar Wulari duk a birnin Maiduguri.

Gwamna Zulum ya bayyana cewa kudirin gwamnatinsa shi ne samar da akalla cibiyar kiwon lafiya a cikin kowace gunduma 312 a jihar Borno, daidai da yadda hukumar lafiya ta duniya (WHO) ta tsara.

Haka zalika kuma, Zulum ya shaidar da cewa, kafin hakan gwamnatinsa ta dauki daruruwan ma’aikatan kiwon lafiya a jihar domin ganin cibiyoyin sun gudana kamar yadda ya dace. Sannan kuma Gwamnan ya bayar da tabbacin sanya kayan aiki ga dukan cibiyoyin kiwon lafiyar da gwamnatin sa ta samar a kowane bangaren jihar hadi da kwararrun ma’aikata.

Dangane da ginin hanyar Maiduguri zuwa Bama, Gwamna Zulum ya sanar da cewa gwamnatin jihar tana tattaunawa da Alhaji Aliko Dangote domin samun tallafi kara tsawon hanyar daga Bama zuwa Banki- da zaran aikin hanyar ya isa garin Bama. Haka kuma ya kara da cewa aikin hanyar zai taimaka wajen bunkasa rayuwar al’ummar yankin.

A katshe, Gwamna Zulum ya yaba da ingancin ayyukan da ya bude, wadanda ma’aikatar kiwon lafiya a jihar ta aiwatar tare da ma’aikayar sake farfado da yankunan da matsalar tsaro ta shafa a jihar.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Amince Da Gina Jami’o’i Masu Zaman Kansu 20

Next Post

Nda-Isaiah Mutumin Kirki Ne, Inji Magajin Garin Nupe

Labarai Masu Nasaba

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

Tukunyar Gas Ce Ta Fashe Ba Bam Ba —Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano

by
8 hours ago
0

...

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

by
9 hours ago
0

...

Yanzu-yanzu: EFCC Ta Cafke Akanta Janar Na Kasa, Ahmed Idris Bisa Zargin Badakala

Yanzu-yanzu: EFCC Ta Cafke Akanta Janar Na Kasa, Ahmed Idris Bisa Zargin Badakala

by Khalid Idris Doya
20 hours ago
0

...

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

by
1 day ago
0

...

Next Post
Garin Nupe

Nda-Isaiah Mutumin Kirki Ne, Inji Magajin Garin Nupe

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: