Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Gabatar Da Naira Biliyan 195 A Matsayin Kasafin 2022

by
6 months ago
in RAHOTANNI
1 min read
Gwamnan Bauchi Ya Gabatar Da Naira Biliyan 195 A Matsayin Kasafin 2022
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Daga Khalid Idris Doya,

Gwamnatin Jihar Bauchi ta gabatar da naira biliyan N195,355,607,143:00 a matsayin kasafin kudin shekara ta 2022 da za a gudanar da manyan ayyuka da sauran fannin gudanar da ayyukan yau da gobe kamar yadda gwamnan Jihar Bala Muhammad ya sanar.

Wannan harsashen kasafin kudin ya kunshi naira biliyan N84,375,180,518 :00 kwatan-kwacin kashi 43 cikin dari da za a kashe wajen gudanar da ayyukan yau da kullum tare da ware naira biliyan N110,620,426,625 :00 kimanin kaso 57 cikin dari wajen gudanar da manyan ayyuka.

Labarai Masu Nasaba

2023: Kotu Ta Yi Fatali Da Karar Emefiele Kan Ministan Shari’a Da INEC

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

Da ya ke gabatar da kasafin a gaban kwaryar Majalisar dokoki jihar a Larabar nan gwamnan Jihar Bala Muhammad ya bayyana cewar wannan Kasafin na 2022 ya yi kasa da kaso 8.5 Idan aka kwakwanta da kasafin 2021 da muke ciki, a cewarsa rage kasafin ya faru ne domin su samu zarafi da damar fuskantar hakikanin halin da ake ciki domin tabbatar da karasa ayyuka ko cigaba da gudanar da ayyukan da suke akwai da wadanda ake son gudanarwa cikin nasara.

ADVERTISEMENT

Ya kuma ce hakan zai basu damar dukkanin ayyukan da aka jero an samu damar gudanar da su a zahirance.
Daga bisani sai ya nemi hadin kan Majalisar dokoki jihar domin samun nasarar ayyukan da gwamnati ta sanya a gaba, ya kuma jinjina musu bisa goyon bayan da suka jima suna baiwa gwamnatinsa.

Da ya ke amsar kasafin, Shugaban Majalisar dokokin jihar, Abubakar Y. Sulaiman, ya bada tabbacin cewa kwamitocin da abun ya shafa za su yi hanzarin gudanar da ayyukan da suke gabansu domin ganin an samu yin aiki kan kasafin domin amincewa da shi don bada damar fara fara amfani da kasafin da wuri.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Sin Ta Shirya Shigar Da Kudade Cikin Ayyukan Kyautata Amfani Da Kwal

Next Post

An Kammala Kacici-Kacicin da CITAD Ta Shirya Ga Daliban Jihar Kano

Labarai Masu Nasaba

2023: Kotu Ta Yi Fatali Da Karar Emefiele Kan Ministan Shari’a Da INEC

2023: Kotu Ta Yi Fatali Da Karar Emefiele Kan Ministan Shari’a Da INEC

by Khalid Idris Doya
2 days ago
0

...

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

Hukumar Alhazan Kogi Ta Fara Shirin Bita Ga Maniyyata

by Ahmed Muhammad Dan'asabe
6 days ago
0

...

Fashewar Gas: An Zakulo Gawarwaki 9 A Ginin Da Ya Rushe A Kano

Fashewar Gas A Kano: Ministar Jinkai Ta Nemi A Dauki Matakan Riga-kafi

by
6 days ago
0

...

Baki Biyu Bai Dace Da Matsayin Amurka Ba

Baki Biyu Bai Dace Da Matsayin Amurka Ba

by CMG Hausa
6 days ago
0

...

Next Post
An Kammala Kacici-Kacicin da CITAD Ta Shirya Ga Daliban Jihar Kano

An Kammala Kacici-Kacicin da CITAD Ta Shirya Ga Daliban Jihar Kano

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: