Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Janye Sunan Sani Damban A Cikin Kwamishinoninsa

by
3 years ago
in Da dimi-diminsa
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Kwana guda da fara tantance Kwamishinonin da gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Muhammad Abdulkadir ya aike wa majalisar dokokin jihar Bauchi domin tantancewa da amincewa da su, kwatsam sai majalisar ta riski wasika daga wajen gwamnan wanda ke bukatar ta amince masa janye sunan mutum guda daga cikin jerin wadanda ya aiko tun a farko.

Gwamna Bala ya cire sunan Dakta Sai Muhammad daga karamar hukumar Dambam a cikin jerin sunayen kwamishinonin da ya zaba gami da sauya shi da wani, inda majalisar kuwa ta amince masa da sauya sunan.

Wakilinmu ya shaida mana cewar a ranar Litinin 2 ga watan Satumba ne gwamnan ya aike da bukatar janye sunan mutum guda daga cikin wadanda ya nemi su zama masa kwamishononi a zangonsa ta farko.

Labarai Masu Nasaba

Zanga-Zanga Ta ɓarke A Asibitin Kwararru Na Gwamnatin Adamawa

Jirgin Kasan Injiniyoyi Ya Halaka Dabbobi 700 A Hanyar Kaduna-Abuja

Sai dai babu cikakken bayani kan dalilin gwamna na daukar wannan matakin.
Da yake yi wa ‘yan jarida karin haske kan wannan matakin, Musa Wakili Nakwanda, mambar majalisar dokokin jihar Bauchi mai wakiltar mazabar Bogoro kana mai magana da yawun majalisar, ya shaida cewar gwamna yana da cikakken ikon turo sunan wanda yake so da janyewa.

A cewar shi; “Gwamnan shi ke da ikon zabar wadanda zai aiko majalisa domin tantancesu, don haka yana da cikakken ikon janye sunan wanda yake son ya janye daga cikin jerin sunansu kwamishononinsa,” A cewar shi.

Wakilinmu ya shaida mana cewar a jiya Talata majalisar ta dauka domin fara tantance Kwamishononin inda ta amince da sunayen mutum goma daga cikin kwamishinonin jihar.

Musa Wakili ya jero sunayen kwamishononin goma da majalisar ta tantance gami da amincewa da su ranar farko, inda ya bayar da sunansu da kamar haka: Farfesa Adamu Ahmad daga qarama hukumar Ningi; Dakta Aliyu Tilde qaramar hukumar Toro; Abdulkadir Muhd Chika Soro, Alkaleri; Umar Abubakar Sade, Darazo; Jidauna Tula Mbami, Bogoro; Hajiya Hajara Itas/Gadau; Dakta Aminu Hassan Gamawa; Turaki Muhammad Manga, Misau; Abdulrazak Nuhu Zaki, Warji; sai kuma Ahmade Aliyu Jalam daga qaramar hukumar Damban, dukkaninsu majalisar ta tantancesu haxi da amincewa da sub a tare da bata wani lokaci ba.

Wakilinmu a majalisar dokokin jihar ta Bauchi, ya shaida mana cewar wasu daga cikin wadanda aka tantance sun fuskanci tambayoyi zafafa daga majalisar jihar, inda wasu kuma tambayoyi masu sauki ne suka riske su, saidai babu guda daga cikin goman da suka tantance wadanda suka ki amince da shi.

Kamar yadda majalisar ta tsara, a yau Laraba ma za ta karasa tantance sauran kwamishinonin da gwamnan yake son su zama masa mukarrabai.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnan Adamawa Ya Tsallake Rijiya Da Baya

Next Post

Nijeriya Ta Janye Jakadanta Daga Afirka Ta Kudu

Labarai Masu Nasaba

Zanga-Zanga Ta ɓarke A Asibitin Kwararru Na Gwamnatin Adamawa

Zanga-Zanga Ta ɓarke A Asibitin Kwararru Na Gwamnatin Adamawa

by Muh'd Shafi'u Sale
2 weeks ago
0

...

Jirgin Kasan Injiniyoyi Ya Halaka Dabbobi 700 A Hanyar Kaduna-Abuja

Jirgin Kasan Injiniyoyi Ya Halaka Dabbobi 700 A Hanyar Kaduna-Abuja

by Abdulrazaq Yahuza Jere
2 weeks ago
0

...

Da ɗimi-diminsa: Gobara Ta Sake Tashi A Babbar Kasuwar Sokoto

Da ɗimi-diminsa: Gobara Ta Sake Tashi A Babbar Kasuwar Sokoto

by Abdulrazaq Yahuza Jere
3 weeks ago
0

...

Wani Abu Da Ake Zargin Bom Ne Ya Jikkata Mutane A Gashuwa

Wani Abu Da Ake Zargin Bom Ne Ya Jikkata Mutane A Gashuwa

by Muhammad Maitela, Damaturu
4 weeks ago
0

...

Next Post
Kyamar Baki: A Maris Babu Dan Nijeriya Da Ya Rasa Ranshi A Afirka Ta Kudu -Ofishin Jakadanci

Nijeriya Ta Janye Jakadanta Daga Afirka Ta Kudu

Leave Comment

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: