Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Gwamnan Bauchi Ya Tallafa Wa Iyalan Wadanda Suka Rasa Rayukansu A Kifewar Kwale-kwale

by
1 year ago
in LABARAI
2 min read
Kiran Da Tsohon Gwamna Shema Na A Dawo Tafiyar PDP Ya Makara –inji PDP A Gyara
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Iyalan mutum 11 da suka rasa rayukansu sakamakon kifewar kwale-kwale a kogin Buji da Garin Dole da ke karamar hukumar Itas Gadau a kwanakin baya sun samu tallafin naira miliyan biyu daga hannun Gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Muhammad domin rage musu radadi.

Shugaban karamar hukumar Alhaji Abdullahi Maigari, shine ya shaida hakan a yayin rabon kudaden ga iyalan wadanda suka rasa ‘yan uwansu sakamakon wannan iftila’in.

Maigari wanda ya shaida cewar kowani mutum daga cikinsu zai samu naira dubu dari (N100,000) na rage radadin halin da suka tsinci kai a ciki, ya kara da cewa al’ummomin da suka samu tallafin su sani ba wai diyyar asarar da suka yi ne aka biya su ba; a’a kawai tallafin rage radadi ne gwamnan ya ba su, sai shawarcesu da su dauki lamarin da ya faru a matsayin mukaddari daga Allah.

Labarai Masu Nasaba

Tukunyar Gas Ce Ta Fashe Ba Bam Ba —Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

A cewarsa cikin kwanaki dari da ya yin a farko a matsayinsa na zabebben shugaban karamar hukumar, an samu aiwatar da muhimman ayyukan da suka dace wajen ganin an inganta rayuwar jama’a da suka kunshi, sashin wutar lantarki, ruwa mai tsafta, lafiya, ilimi, tallafa wa kungiyoyi, da agazawa kungiyoyin addinai tare da ‘yan kasuwa domin rayuwa take ingantuwa.

Da ya ke jawabi yayin rabon tallafin, Malam Magaji Gwaram ya nuna matukar godiyarsu ga gwamnan a bisa wannan tallafin da ya bayar, sai ya nemi wadanda aka ba su tallafin da su yi kokarin yin amfani da dukiyoyin ta hanyoyin da suka dace domin inganta rayuwarsu da na iyalansu lura da cewa da ‘yan uwansu na ciki za su ci gaba da aza musu, sai dai ya ce dukkanin abun da ya faru mukaddari ne daga Allah.

Idan za ku iya tunawa dai, jama’a 18 ciki har da iyaye mata ne suka rasa rayukansu sakamakon tsautsayin da ya faru na kifewar jirgin ruwa a cikin kogin Buji.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Rashin Iyan Bashir: Babban Gibi Ne In ji Ya Salaam

Next Post

Fadar Shugaban Kasa Ta Gargadi Masu Yunkurin Batanci Ga Buhari

Labarai Masu Nasaba

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

Tukunyar Gas Ce Ta Fashe Ba Bam Ba —Kwamishinan ‘Yan Sandan Kano

by
6 hours ago
0

...

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

Wani Bam Ya Fashe A Sabon Garin Jihar Kano

by
7 hours ago
0

...

Yanzu-yanzu: EFCC Ta Cafke Akanta Janar Na Kasa, Ahmed Idris Bisa Zargin Badakala

Yanzu-yanzu: EFCC Ta Cafke Akanta Janar Na Kasa, Ahmed Idris Bisa Zargin Badakala

by Khalid Idris Doya
19 hours ago
0

...

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

Jami’an Tsaro Sun Kama Buduwar Da Ta Yi Batanci Ga Fiyayyen Halitta A Maiduguri

by
24 hours ago
0

...

Next Post
Fadar Shugaban Kasa Ta Gargadi Masu Yunkurin Batanci Ga Buhari

Fadar Shugaban Kasa Ta Gargadi Masu Yunkurin Batanci Ga Buhari

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

Go to mobile version
%d bloggers like this: