Khalid Idris Doya">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Gwamnan Gombe Ga ‘Yan Karkara: Ku Kare Makamashin Lantarkin Hasken Rana Da Ake Muku

by Khalid Idris Doya
February 12, 2021
in LABARAI
3 min read
Gwamnan Gombe Ga ‘Yan Karkara: Ku Kare Makamashin Lantarkin Hasken Rana Da Ake Muku
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Gwamnan jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya hori al’ummar yankunan karkara na jihar su sanya ido tare da kare aikin makamashin hasken lantarki ta makamashin hasken rana da ake musu don amfanin kansu.

Ya yi kiran ne a yayin kaddamar da aikin samar da wutar lantarki daga hasken rana mai karfin Kilowatt 85 a kauyen Dakkiti na karamar hukumar Akko.
Gwamnan ya kaddamar da aikin ne tare da babban Manajan Daraktan hukumar samar da wutar lantarki a yankunan karkara ta kasa (REA), Ahmed Salihijo Ahmed.
Wakilinmu ya nakalto cewa, Gidauniyar Gwamnatin tarayya kan samar da wutar lantarki a karkara (REF) ce ta gudanar da aikin, karkashin hukumar samar da Wutar Lantarki a yankunan karkara REA.

samndaads

Gwamna Inuwa ya ce aikin alhaki ne na hukumar wanda ya dace da shirin Gwamnatin tarayya na kyautata rayuwar ‘yan Nijeriya da nausa ta gaba ta fuskar inganta wutar lantarki ga ‘yan Nijeriya, musamman ma wadanda ke zaune a yankunan karkara, yana mai fatan za a fadada irin wannan aikin zuwa sauran sassan jihar, kamar yadda wata sanarwar da Daraktan yada labaran gidan gwamnatin jihar, Ismaila Uba Misilli ta nakalto.

Inuwa na cewa, “Gwamnatinmu tana aiki kafada da kafada da Gwamnatin tarayya da sauran hukumomi da dama don tabbatar da samar da ababen more rayuwa ga jama’a, musamman wadanda ke zaune a yankunan karkara”.

Sai ya ba da tabbacin cewa al’ummar jihar ba kawai za su goyi bayan wannan aikin ba ne, har ma za su marawa duk wasu ayyukan samar da lantarki, domin tabbatar da nasarar samar da dauwamammiyar wutar lantarki.

Gwamnan ya yi imanin cewa aikin zai yi tasiri wajen inganta rayuwar al’ummar yankin, “Ina yaba wa Gwamnatin Tarayya ta hanyar ma’aikatar Makamashi da kuma hukumar samar da lantarki a Karkara bisa jajircewa da gudummawar da suke bayarwa wajen samar da wutar lantarki ga al’ummomin mu mazauna karkara, muna ganin wannan kokarin naku a duk fadin kasar nan”.

Ya kuma bukaci al’ummar yankin su dauki aikin a matsayin nasu ta hanyar kiyaye shi daga mabarnata tare da tabbatar da suna biyan kudin wutar akan lokaci.

Gwamnan sai ya tabbatar wa al’ummar jihar cewa gwamnati mai ci za ta ci gaba da samar da ababen more rayuwa ga mazauna karkara, musamman ganin cewa sama da kaso 75 cikin dari na al’ummar jihar suna zaune ne a yankunan karkara.

Manajan Darakta kuma shugaban hukumar samar da wutar lantarkin a karkara, Ahmed Salihijo Ahmed, ya ce kamar yadda shugaban kasa Muhammadu Buhari ya sahale mata, hukumarsa ce ke da alhakin samar da makamashi ga al’ummomin Nijeriya da ba su da wutar ko basu wadatacciyar ta.

Ya ce an samu nasarar aiwatar da aikin ne a karkashin asusun samar da lantarki a Karkara wanda aka faro shi don tabbatar da daidaito wajen samarwa da rarraba wutar lantarki a fadin kasar nan.

Shugaban karamar hukumar Akko, Abubakar Barambu, ya ce bisa samar da wannar wuta ga al’ummar Dakkiti, a yanzu jama’ar kauyen za su iya morar alfanun da duk ake samu daga wutar lantarki ta fuskar ci gaban tattalin arziki.

“Ya ce ku sani cewa mun yi wannan aikin ne na Dakkiti bisa kyakkyawan tsari da bin ka’idojin kasa da kasa wajen kafa wannar karamar tashar wutar lantarki da aka girka kana mai karfin Kilowatts 85 wanda ya kunshi farantai masu tattara hasken rana guda 100, da batura 96 da kuma Injin Janareta mai karfin KbA 30.

Sarkin Gona, wanda ya samu wakilcin Ajiyan Gona, Alhaji Abubakar Usman, ya gode wa hukumar samar da lantarkin a yankunan karkara kan wannan karamci na gwamnatin tarayya tare da kara godewa gwamnati mai ci ta Gwamna Muhammad Inuwa Yahaya ke yi bisa jajircewa wajen tabbatar da gudanar da aikin a kan lokaci.

SendShareTweetShare
Previous Post

Yawaitar Hadurra: Matsalolin Da Suka Kamta A Duba

Next Post

Babu Rabuwar Kai A Tsakanin `Yan APC A Karamar Hukumar Lere – Abubakar Buba

RelatedPosts

Hadiza Usman

Hadiza Bala Usman Ta Yi Ta’aziya Ga Iyalan Marigayi Dikko Inde

by Khalid Idris Doya
3 mins ago
0

Daga Abdullahi Sheme A ranar juma'ar da ta gabatane shugabar...

Masana Sun Yaba Wa Shugaba Buhari Kan Sake Nada Hadiza Bala Usman Shugabar NPA

Masana Sun Yaba Wa Shugaba Buhari Kan Sake Nada Hadiza Bala Usman Shugabar NPA

by Khalid Idris Doya
10 mins ago
0

Daga Bello Hamza, Abuja Masana da masu ruwa da tsaki...

An Sako Daliban Da Aka Sace A Zamfara

An Sako Daliban Da Aka Sace A Zamfara

by Khalid Idris Doya
1 hour ago
0

Rahotanni daga jihar Zamfara sun tabbatar da cewa an ceto...

Next Post
Babu Rabuwar Kai A Tsakanin `Yan APC A Karamar Hukumar Lere – Abubakar Buba

Babu Rabuwar Kai A Tsakanin `Yan APC A Karamar Hukumar Lere - Abubakar Buba

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version