Khalid Idris Doya">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Gwamnan Gombe Ya Nuna Kaduwa Da Rasuwar Gwamnan Mulkin Soja Na Farko A Jihar Arewa Maso Yamma

by Khalid Idris Doya
December 21, 2020
in RAHOTANNI
2 min read
Gwamnan Gombe
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Gwamnan Jihar Gombe Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, ya bayyana kaduwa da jimaminsa bisa rasuwar dattijo, tsohon gwamnan jihar tsohuwar jihar Arewa Maso Yamma Alhaji Usman Faruk, Jarman Gombe.

Wakilinmu ya nakalto cewa, marigayi Usman Faruk dai tsohon kwamishinan ‘yan sanda ne, ya rasu ne a ranar Juma’a 18 ga watan Disamba bayan doguwar jinya da yayi fama da shi. An haifesa ne a shekarar 1935 a garin Gombe, ya zama gwamnan mulkin soja ne a yayin mulkin shugaban kasa a zamanin soja Yakubu Gowon

samndaads

Gwamnan ya jagoranci tawagar gwamnatin da ta halarci jana’izar marigayin wanda aka yi a masallacin Modibbo Bubayero dake fadar mai martaba Sarkin Gombe.

A sakon sa na ta’aziyya da ya fitar ta hannun Kakakinsa, Ismaila Uba Misilli, gwamna Inuwa ya bayyana marigayi tsohon kwanishinan ‘yan sandan a matsayin mutum mai cikakkiyar kima, jami’in tsaron da ya yi fice, wanda ya sadaukar da komai na shi don tabbatar da hadin kai da ci gaban Nijeriya, wanda kuma ya bar kyakkyawan abun tunawa da shi tsawon lokaci.

“Za mu yi ta tunawa da shi a matsayin shi na uba da nagartattun ayyukansa lokacin da ya ke cikin damara da bayan ritayarsa, musamman jajircewarsa ga hidimar al’umma, Jihar Gombe da Nijeriya baki daya a matakai daban-daban.

“A madadin gwamnati da al’ummar Jihar Gombe, muna mika cikakkiyar ta’aziyyar mu ga iyalansa da abokai bisa wannan babban rashi. Allah ya yi masa sakayya da Aljannah Firdausi.”

SendShareTweetShare
Previous Post

Rasuwar Nda-Isaiah Rashi Ne Ga Duniyar ’Yan Jarida – Sakataren Masu Saida Jarida Na Kano 

Next Post

Jira Kawai Mu Ke A Ba Mu Damar Farautar Boko Haram – ’Yan Sintirin Borno

RelatedPosts

DATA

Har Yanzu Ana Sayar Da (DATA) Kan Tsohon Farashi Duk Da Ragin Kashi 50

by Khalid Idris Doya
48 mins ago
0

Yawancin masu amfani da layin sadarwa sun ce har yanzu...

Farfesa Dadari

Yawan Karbo Bashin Da Gwamnati Ke Yi Bai Da Amfani Ga Kasar Nan -Farfesa Dadari

by Khalid Idris Doya
53 mins ago
0

Wani Malami a Jami'ar Ahmadu Bello da ke Zaria, Farfesa...

Gobara Ta Yi Sanadiyyar  Mutuwar Uwa Da ‘Ya’yanta Biyu A Kirfi

Gobara Ta Yi Sanadiyyar  Mutuwar Uwa Da ‘Ya’yanta Biyu A Kirfi

by Khalid Idris Doya
1 hour ago
0

Ibtila’in gobara ya ci rayuwar mutum uku daga ciki har...

Next Post
’Yan Sintirin Borno

Jira Kawai Mu Ke A Ba Mu Damar Farautar Boko Haram – ’Yan Sintirin Borno

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version