Khalid Idris Doya">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Gwamnan Gombe Ya Raba Injunan Ban Ruwa Ga Manoman

by Khalid Idris Doya
January 2, 2021
in LABARAI
2 min read
Gwamnan Gombe
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Gwamnan Jihar Gombe Alhaji Muhammadu Inuwa Yahaya, ya kaddamar da Motoci da Babura da za a rabawa jami’ai da ma’aikatan sanya ido kan shirin kyautata rayuwan, da kuma Injunan ban ruwa ga manoman na rani.

 

samndaads

Shirin tallafin, hadin gwiwa ne tsakanin gwamatin jihar da shirin na inganta noma da samar da tallafin kyautata rayuwa da ake kira (IBSDLEIP) a takaice, wanda ke karkashin kulawar bankin bunkasa ci gaban Afirka don tallafawa mata da matasa da gajiyayyu.

 

 

Sai ya bayyana farin ciki kan shirin, ya na mai cewa ci gaba abu ne da ake tsarawa da takamammiyar manufa ta bunkasa rayuwar al’umma musamman ma na yankunan karkara.

 

Ya ce, “Jama’ar mu da suka dogara ga har kar noma sun kai kaso 75 cikin dari na yawan al’ummarmu, don haka duk wani yunkuri na kyautata wannan sashi zai kance mai gwaggwaban tasiri akan jama’ar mu”.

 

“Wannan shi ne dalilin da ya sa gwamnatinmu ta sanya azama sosai wajen aiwatar da wannan shiri, ta hanyar bada nata kason gudunmowa saboda sanin tasirin da zai yi ga mata da matarsa da marassa galihu.”

 

 

Don haka, “Ina shawartar wadanda za su kula da wadannan Motoci da Babura dama wadanda za su ci gajiyar wannan tallafi na Injunan ban ruwa da sauran kayan aiki, su tabbatar sun yi amfani da su yadda ya kamata, musamman ma wadannan motoci da suka kasance masu jan hankalin bata gari”.

 

Ya kara da cewa dole ne masu cin gajiyar wannan shiri su jajirce don ganin jama’ar jihar sun ci gajiyar wadannan kayayyaki.

 

Sai ya bada tabbacin gwamnatin sa na ci gaba da zakulo shirye-shirye da aiwatar da ayyukan da za su amfani al’ummar jihar.

 

A na shi tsokaci, Kwamishinan ruwa na jihar, Mijinyawa Yahaya, ya ce za a yi amfani da Motoci da Baburan ne wajen sanya ido kan aiwatar da shirin a jihar Gombe wanda aka sanya hanu akansa tun shekara ta 2016 amma aka yi watsi rashi saboda rashin kyakkyawar gudanarwa.

 

Ya ce sake farfado da shirin, na nuni da kyakkyawan jagorancin gwamna Inuwa wajen tafiyar da al’amuran jihar yadda ya kamata.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Kana Nan Kungiyoyi Sun Bawa Real Madrid Wahala A Shekarar 2020 Data Wuce

Next Post

Za Mu Ci Gaba Da Daga Darajar Noma A Oyo, Inji Gwamna  Seyi

RelatedPosts

Kananan Hukumomin Jihar Kano

Yau Za A Yi Karon Batta A Zaben Kananan Hukumomin Jihar Kano

by Khalid Idris Doya
21 mins ago
0

 Jam’iyyu 11 ne za su fafata PDP Kwankwasiyya ta ce,...

Sojoji

Tsofaffin Sojoji Sun Nemi Karin Kudin Fansho

by Khalid Idris Doya
33 mins ago
0

Kungiyar tsofaffin sojoji ta kasa reshen jihar Anambra ta bukaci...

Ali Baba

Zaben Kananan Hukumomi: PDP Kwankwasiyya Ta Maka KASEIC A Kotu

by Khalid Idris Doya
49 mins ago
0

Bangaren Kwankwasiyya na jam'iyyar PDP a jihar Kano, ta jadadda...

Next Post
Gwamna  Seyi

Za Mu Ci Gaba Da Daga Darajar Noma A Oyo, Inji Gwamna  Seyi

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version