Hussaini Yero">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Gwamnan Zamfara Ya Sake Kubutur Da Mutane 11 Daga Masu Garkuwa

by Hussaini Yero
November 25, 2020
in RIGAR 'YANCI
2 min read
APC Zuwa PDP
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Gwamnan jihar Zamfara, Dakta Bello Mohammed Matawalle, ya taimaka wajen ganin an ceto mutane 11 da a ka yi garkuwa da su ba tare da biyan kudin fansa ba.

Sakataren yada labarai na Gwamnan na Zamfara, Alhaji Jamilu Iliyasu Birnin-Magaji ya bayyana haka a takardar da yasanya mahannu ya rabawa manema lararu a Gusau babban birnin jihar Zamfara.

samndaads

Da ya ke karbar wadanda lamarin ya rutsa da su, maza 10 da mace daya wadanda suka fito daga Karamar hukumar Bukkuyum ta jihar, gwamnan Matawale,ya bayar da tabbacin cewa, gwamnatinsa ba za ta huta ba har sai an samu cikakken zaman lafiya a dukkan sassan jihar.

Matawalle ya kara da cewa, kudirinsa shi ne tabbatar da dorewar zaman lafiya a duk sassan jihar da ma wasu sassan.dan samun dauwamammen zaman lafiya da tsaro a jihar.kuma yarjejeniyar zaman lafiya da sasantawa tare da ‘yan fashi da suka tuba za ta dmdore yayin da wadanda suka ki tuba kuma suka ki ajiye makamai za su gamu da fushin doka.

Tun da farko, yayin mika mutanen da aka sace su 11 ga gwamnan, kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar, Alhaji Abubakar Muhammed Dauran ya ce,an kubutar da mutanen ta hanyar tattaunawar ba tare da biyan wadanda suka sace su kucin fansa ba.

Wadanda aka kubutar sun nuna matukar farin ciki da godiya ga gwamna Matawalle wanda suka bayyana a matsayin mai son samar da zaman lafiya da kuma kaunar dukkanin bangarorin mutane a jihar.

Idan ba a manta ba a ranar Alhamis din da ta gabata ne Gwamna Matawalle ya gudanar da wani taro kan tsaro tare da dukkanin masu ruwa da tsaki daga karamar hukumar Bukkuyum domin tattaunawa kan hanyoyin da za a bi wajen samar da zaman lafiya da lumana a jihar.

SendShareTweetShare
Previous Post

Ganduje Ya Nada ‘Yan Kwamitin Gudanarwar Sabbin Asibitocin Kwararru Na Kano

Next Post

Adamawa Ta Gabatar Da Naira Biliyan 140 A Matsayin Kasafin Kudin 2021

RelatedPosts

Marayu

’Yan Bindiga Sun Sace Marayu Bakwai A Gidan A Marayun Abuja

by Hussaini Yero
20 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Akwai dan dsoro na alamun tashin...

Bogi Wiwi

Legas: An Cafke Dan Sandan Bogi Da Wiwi

by Hussaini Yero
20 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Rahotanni daga Jihar Legas, sun zo...

Aguda

Mutum Ya Rasu A Arangamar Matasan Unguwar Aguda Dake Surulere

by Hussaini Yero
20 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, An tabbatar da mutuwar mutum daya...

Next Post
Adamawa

Adamawa Ta Gabatar Da Naira Biliyan 140 A Matsayin Kasafin Kudin 2021

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version