Gwamnati Za Ta Farfado Da Rukunin Gidaje Masu Saukin Kudi 46 A Nijeriya
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnati Za Ta Farfado Da Rukunin Gidaje Masu Saukin Kudi 46 A Nijeriya

byAbubakar Abba
2 years ago
Gidaje

Bankin da ke bayar da lamunin gina gidaje na kasa wato FMBN, ya kirkiro da aikin gyaran ayyukan gidajen da aka yi wasti da su kimanin 46 a daukacin fadin Nijeriya.

Domin bankin ya cimma wannan kudurin na sa, ya yi hadaka da bankin bunkasa Afrika na gina gidaje wato (ADB).

  • Bata Gari Sun Daka Wa Motar BUA Wawa A Kan Hanyar Zariya
  • An Fara Gudun Yada-kanin-wani A Gasar Firimiya

Bankin na ADB dai, ya kasance wata cibiyar bayar da daukin kudade ne da ke bayar da goyon baya wajen gina rukunin gidaje a Afrika.

Manajin Darakta na banin FMBN Shehu Usman Osidi ne ya bayyana hakan a kwanan baya a Abuja, lokacin da ya karbi bakuncin mahukutan bankin na ADB.

A caewar Shehu, bankin na FMBN na bayar da fifiko wajen sake farfado da rukunin gidaje da ke a fadin kasar nan.

Ya kara da cewa, bisa kara karfafa hadar zata taimaka wajen gina gidaje da kuma samar da rance ga masu gina rukunin gidaje a Nijeriya.

Shehu ya ci gaba da cewa, a Nijeriya a jihohi 36 akwai ayyukan gidaje sama da 46 da aka yi watsi da su, wadanda bankin na FMBN ya kudiri aniyar gyransu

Ya ci gaba da cewa,“Bincike ya nuna cewa, wasu bankuna sun kulla yarjajeniyar da jihohi yarjajeniyar domin bayar da kudade don gina gidaje, wanda ake sa ran jihohin za su samar da kayan aiki domin gina rukunin gidaje”.

Sai dai, Shehu ya ce, amma abun takaici akasarin jihohin sun gaza cika alkawuransu, wanda hakan ya janyo aka yi watsi da ayyukan na gina gidajen a jihohin su.

Shehu ya ce,“ Mun mun tuntubi bankin na ADB, wanda muka gano cewa, suna bayar da kudade, a saboda hana, mun shigo da su don su bayar da kudade don fara aikin farfado da ayyukan na gina gidajen don sayar da su ga ‘yan Nijeriya masu bukata”.

Ya kara da cewa, Nijeriya ce ta biyu da ke da hannun jari a bankin wanda ya kai kimanin kashi 15, wanda hakan zai bamu damar yin dubi kan yadda za a samar da kudade domin mu cimma burin mu na gina gidaje 100,000 ga ‘yan Nijeriya a 2024.

Ya ce, a yanzu bankin na FMBN na kan nazari kan yarjejeniyar da aka kaulla aka kuma yi watsi da ita kuma manufar ita ce domin amfanin ‘yan Nijeriya.

A na sa jawabin, shugaban bankin na ADB Thierno-Habib Hann ya ce, bankin na ADB ya zo Nijeriya ne wanzar da ajandarsa ta samar da kudaden bunkasa gidaje, wanda kuma ya gano cewa, Nijeriya masauki ce ta zuba jarin da ya kai sama da dala biliyan 25bn a duk shekara.

A cewarsa,“ A shirye muke mu yi hadaka da bankin FMBN da kuma sauran cibiyoyin da ke Nijeriya don mu cike gibin da ake da shi, na karancin gidaje, inda ya kara da cewa, kalubalem suna nan har da damar”.

A cikin wani kundin ta mika ragamar shugabanci da wakilinmu ya samu, tsohon Manajin Darakta na bankin FMBN Madu Hamman ya ce, shirin aikin gina giaje na NHF, bankin FMBN ne ya kirkiro da shi don ci gaba da gina gidaje a cikin saukin kudi ta hanyar zuba jari na dogon zango wanda za a rinka cire kashi 2.5, daga cikin albashin ma’aikata.

Madu ya kara da cewa, wasu daga cikin ci gaba da aka samu a watanni 12 da suka wuce a karo na farko a 2023, daukin kudaden da aka karbo sun dara Naira biliyan 100.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama
Tattalin Arziki

Bayan Shekara 20 Nijeriya Ta Sake Dawo Da Tsarin Bayar Da Hayar Kananan Jiragen Sama

October 3, 2025
Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho
Tattalin Arziki

Tashoshin Jiragen Ruwa Sun Samar Da Kashi 19.6 Na Fitar Da Kayan Da Ba Su Shafi Mai Ba—Dantsoho

October 3, 2025
Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG
Tattalin Arziki

Majalisar Wakilai Za Ta Sasanta Dangote Da NUPENG

September 27, 2025
Next Post
Mutum 6 Sun Kamu Da Cutar Sanƙarau A Bauchi

Mutum 6 Sun Kamu Da Cutar Sanƙarau A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version