Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home LABARAI

Gwamnatin Bauchi Na Kashe Fiye Da Naira Biliyan Guda Kowane Wata Kan Kiwon Lafiya

by Muhammad
April 4, 2021
in LABARAI
2 min read
Gwamnan Bauchi
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Khalid Idris Doya,

Gwamnan jihar Bauchi, Sanata Bala Mohammed ya nuna takaicinsa na cewar, duk da makudan kudade da gwamnatin jihar take kashewa na fiye da naira biliyan guda a kowane wata kan kiwon lafiya tun daga tushe, ma’aikatan kiwon lafiya a karkashin wannan shiri ba su zuwa wuraren ayyukan su a cibiyoyin kiwon lafiya daban-daban da suke fadin jihar.

Ya fahimci cewar, ma’aikatan sa kai kan lamuran kiwon lafiya su ne ala-kulli halin suke bakin ayyuka, ba ainihin ma’aikata ba, dalilin da ya sa kenan gwamnati take fafitikar neman kudade domin daukar wadannan ma’aikatan wucin-gadi ko nasa kai.

Gwamnan yana jawabi ne  a wata cibiyar kiwon lafiya dake cikin garin Azare, yayin da yake cigaba da buda ayyukan cigaba dake sassan jihar Bauchi, inda yake cewar, gwamnati za ta yi amfani da ‘yan kudade dake raritar ta domin tura wadannan ma’aikatan sa kai zuwa makarantar koyon ayyukan kiwon lafiya, domin samun cancantar daukar su aiki a cikin gwamnati.

Ya ce, “Ina matukar farin ciki da yadda wadannan ma’aikatan sa kai suke gudanar da ayyuka a cibiyoyin kiwon lafiya, a yayin da ainihin ma’aikata suke yin sakaci da ayyukan su. Don haka nake jan hankali wadannan ma’aikata na wucin-gadi da su cigaba da gudanar da ayyuka, tare da basu tabbacin cewar, bada jimawa ba, za mu dauke su aiki na dindindin.”

Sanata Bala Mohammed ya kuma ba su tabbacin cewar, gwamnati za ta yi dukkan mai yiwuwa domin samun rarar kudade da zai bada damar daukar su ayyukan gwamnati na din-din-din, yana mai cewar, “Mun tafi sarmadan akan wannan niyya domin cimma manufar samar da ayyukan yi wa wadannan ma’aikata masu kishin jiha”.

Ya kuma kara tabbatar wa wadannan ma’aikatan kiwon lafiya da cewar, “Bada jimawa ba, za mu daidata muku tsarin albasu a cikin ayyukan gwamnati, domin a halin yanzu muna nan muna share ma’aikatan bogi dake hana ruwa gudu. Kuma muna nan kan wannan fafitika na share ma’aikatan bogi cikin kankanin lokaci, biyo bayan wani kwamiti da muka kafa karkashin jagorancin Mukaddashin gwamnan jiha, Sanata Baba Tela.

Dangane da wannan manufa ce, gwamnan ya umarci kwamishinan lafiya na jihar domin ya yi kididdigar yawan wadannan ma’aikata nasa kai da zumma share masu fagen zuwa makarantar koyon aikin likitanci kan hanyar su ta zamowa sahihan ma’aikatan gwamnatin jihar Bauchi.

A gefe guda, gwamnan ya bayyana cewar gwamnatinsa ta samu nasarar sake kudaden hadaka da kungiyoyin tallafi wanda hakan ya bada damar samar da manyan da kananan asibitocin kula da lafiya a fadin jihar, tare da maida hankali wajen biyan kudaden hadaka a fannoni kula da lafiyar yara da Mata domin rage yawaitar mace-macen jarirai a lokacin haihuwa.

SendShareTweetShare
Previous Post

Tabarbarewar Tsaro: Me Yake Faruwa Da ‘Yan Nijeriya?

Next Post

PDP Da Ndume Sun Nuna Damuwarsu Kan Faduwar Jirgin Sojoji

RelatedPosts

Kogi

‘Yan Bindiga Sun Sace Ma’aikatan Jinya Biyu A Kaduna, Matafiya 18 A Oyo

by Muhammad
34 mins ago
0

Kwanaki biyu da sace daliban jami'ar Greenfield da ke jihar...

Sace Daliban Jami’a A Kaduna: Yadda ‘Yan Bindiga Suka Shammaci Jami’an Tsaro

Sace Daliban Jami’a A Kaduna: Yadda ‘Yan Bindiga Suka Shammaci Jami’an Tsaro

by Sulaiman Ibrahim
5 hours ago
0

Daga Abubakar Abba, Kaduna A daren ranar Talata da dare...

Gwamnan Gombe Ya Nuna Takaicinsa Kan Masu Gina Gidajen Mai A Unguwanni

Gwamnan Gombe Ya Nuna Takaicinsa Kan Masu Gina Gidajen Mai A Unguwanni

by Sulaiman Ibrahim
5 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya, Gombe Gwamnan Jihar Gombe, Alhaji Muhammadu...

Next Post
NAF

PDP Da Ndume Sun Nuna Damuwarsu Kan Faduwar Jirgin Sojoji

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version