Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Gwamnatin Bauchi Ta Raba Kayyakin Dakile Zazzabin Cizon Sauro A Asibitoci 100

by Tayo Adelaja
September 14, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Khalid Idris Doya, Bauchi

Gwamnatin Jihar Bauchi karkashin gwamnan jihar Muhammadu Abdullahi Abubakar ta fara rabon magangunan zazzabin cizon sauro, gidajen sauro da kuma kayayyakin gwaje-gwajen zazzabin cizon sauron ga cibiyoyin kiwon lafiya guda 100 da suke fadin kananan hukumomi 20 na Jihar Bauchi.

samndaads

Rabon kayan wanda ya gudana a karkashin hukumar BACATMA da hadin guiwar babban bakin duniya na shirin ceto rayukan mutune miliyan guda a jihar.

Da yake yi wa LEADERSHIP  A Yau karin bayani kan rabon, babban Sakatare a hukumar yaki da zazzabin cizon sauro, tarin fuka, cuta mai karya garkuwar jiki na jihar Bauchi (BACATMA), Dakta Masur Mustapha Dada ya bayyana cewar a ranar Litinin din da ta gabata ne suka kaddamar da fara rabon kayyakin zazzabin cizon sauron da magungunan domin kare lafiyan al’umman Jihar Bauchi.

Dakta Dada ya cigaba da bayyana cewa a kowace karamar hukuma sun zabi asibitoci guda biyar ne, inda asibiti kwara daya cur ne a dukkanin fadin kananan hukumomin jihar Bauchi 20 da ake da su “Yanzu haka ana ci gaba da rabon wannan maganan a fadin jihar, kuma ana raba su kyauta ne, idan mutum ya zo asibiti yana zazzabi za a basa magani kyauta ne, gwajin da za a yi maka kyauta ne, kuma idan aka tabbatar mutum yana da zazzabin cizon sauro shi ma kyauta muke baiwa mutum maganin”. Inji Daktan Dada

Daktan ya ce, shi kuma gidan sauro ba kowa da kowa suke rabawa ba sai wanda ya cancanta “Shi gidan sauro ba kowa da kowa ake bayarwa ba, akwai yara y’an kasa da shekara daya ana basu gidan sauro daya, matan da suke cikin shekarun haihuwa suma ana basu, da zarar ta fara zuwa awo a wannan lokacin zamu dauki kwara daya mu bata. Yanzu haka kowani mataniti mun basu gidajen sauro biyu-biyu”.

SendShareTweetShare
Previous Post

Orabe Philips: Matashin Da Ya Rafke Ba’amurke Da Tabarya

Next Post

Likitoci Sun Bayyana Illolin Hayakin Taba Ga Hanyoyin Jinin Huhu

RelatedPosts

Makiyaya Ondo

Korar Makiyaya A Ondo: Cikakken Rahoton Yadda Ta Kaya Taron Gwamnoni Da Shugabannin Fulani

by Muhammad
1 day ago
0

Daga Khalid Idris Doya, Gwamnonin Nijeriya sun kira taron gaggawa...

Kasafin 2021

Hotunan Sabbin Shugabannin Rundunonin Tsaro

by Sulaiman Ibrahim
2 days ago
0

Major-Gen. Leo Irabor, Chief of Defence...

Garban

Garban Kauye Farawa Ne Allurar Dinke Barakar Kumbotso – Muslihu Yusuf Ali

by Muhammad
3 days ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, An bayyana zaben Sabon shugaban Karamar...

Next Post

Likitoci Sun Bayyana Illolin Hayakin Taba Ga Hanyoyin Jinin Huhu

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version