Leadership News Hausa
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership News Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Buhari Za Ta Fara Bayyana Zirga-zirgar Kudaden Da Take Kashewa Ta Intanet

by
2 years ago
in LABARAI
2 min read
Gwamnatin Buhari Za Ta Fara Bayyana Zirga-zirgar Kudaden Da Take Kashewa Ta Intanet
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram
ADVERTISEMENT

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya umarci babban akanta na kasa da ya dinga bayyana wa ‘yan Nijeriya adadin kudaden da suke shiga lalitar gwamnatin tarayya da wanda ke fita daga lalitar a kullum.

Shugaba Buhari ya ba da wannan umarni ne a ranar Litinin, 9 ga watan Disamba yayin taron kaddamar da dokoki da tsare-tsaren fayyace hada-hadar kudi na gwamnatin tarayya, inda ya umarci babban akantan ya wallafa rahoton duk wani kudi da aka bai wa kowacce hukuma da ma’aikata da ya haura naira miliyan 10.

Jaridar Premium Times ta ruwaito shugaba Buhari wanda ya samu wakilcin karamin ministan Neja Delta, Tayo Alasoadura ya ce rahoton ofishin babban akantan Nijeriya ne zai dinga sanar da ‘yan Nijeriya adadin kudaden da gwamnati ta bai wa hukumominta da ma’aikatunta domin su gudanar da ayyuka, da kuma sanin adadin kudin da ya shigo musu.

Labarai Masu Nasaba

‘Yan Bindigar Da Suka Sace Daliban Kwaleji 4 A Kaduna Sun Bukaci Kudin Fansa

Gwamnatin Ganduje Ta Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 A Kano

Wakilin Buhari ya ce manufar tsarin shi ne baje ta a faifai kowa ya gani tare da yin keke da keke a harkar tafiyar da kudaden al’umman Nijeriya ba tare da wani boye-boye, kumbiya-kumbiya, lumbu-lumbu ko muna-muna ba.

Bugu da kari, shugaban kasa ya ce bayanin da za’a dinga wallafawa zai kunshi musabbabin bayar da kudin ko kashe kudin, adadin kudin da kuma wanda ya biya kudin ko aka biya kudin, sa’annan sabon tsarin ya tilasta ma hukumomi da ma’aikatu su tabbatar da wallafa duk wata harkallar kudi da ta haura naira miliyan 5.

Haka zalika Buhari ya umarci dukkanin hukumomi da ma’aikatun gwamnati su wallafa yanayin aiwatar da kasafin kudinsu a kowanne kwanaki 7 na karshen kowanne wata, inda bayaninsu zai hada da ayyukansu da kuma amfanin da suka kara ma tattalin arzikin kasar.

Baya ga wallafa kudaden da suka shigo ma gwamnati da wanda suka kashe, shugaba Buhari ya umarci babban akanta na kasa ya dinga wallafa matsayin asusun gwamnati bayan kowanne watanni 4, sa’annan a karshen shekara ma haka.

Like this:

Like Loading...
SendShareTweetShare
Previous Post

Muna Samun Kyakkyawan Jagoranci A Kasuwar ‘Yan Gwari Ta Mile 12 Legas

Next Post

Harkar Ilimi Shi Ne Kan Gaba Cikin Kasafin 2020 A Adamawa  -Dabari

Labarai Masu Nasaba

2023: Kwamishinonin Ganduje 7 Da Ya Amince Da Ajiye Aikinsu Da Ukun Da Ya Yi Watsi Da Su

‘Yan Bindigar Da Suka Sace Daliban Kwaleji 4 A Kaduna Sun Bukaci Kudin Fansa

by Abubakar Abba
12 mins ago
0

...

Gwamnatin Ganduje Ta Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 A Kano

Gwamnatin Ganduje Ta Kaddamar Da Aikin Gina Gidaje 500 A Kano

by Abdullahi Muh'd Sheka
53 mins ago
0

...

‘Yan Arewa Masu Kai Abinci Yankin Inyamurai Su Dakatar Saboda Kisa –Matasan Arewa A Kudu

‘Yan Arewa Masu Kai Abinci Yankin Inyamurai Su Dakatar Saboda Kisa –Matasan Arewa A Kudu

by
7 hours ago
0

...

EFCC Ta Bankado Gidaje 17 A Nijeriya Da Kasashen Waje Na Akanta Janar

EFCC Ta Bankado Gidaje 17 A Nijeriya Da Kasashen Waje Na Akanta Janar

by
19 hours ago
0

...

Next Post
Harkar Ilimi Shi Ne Kan Gaba Cikin Kasafin 2020 A Adamawa  -Dabari

Harkar Ilimi Shi Ne Kan Gaba Cikin Kasafin 2020 A Adamawa  -Dabari

Domin bayar da talla ko neman ƙarin bayani a tuntuɓe mu a: +2348039216372

  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us | English Edition | Fashion Magazine | Business News

© 2022 Leadership Media Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2022 Leadership Media Group .

%d bloggers like this: