Gwamnatin Ce Ta Harzuka Wanda Suka Sace Mu, Suka Fara Dukanmu -Wanda Ya Kubuta
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Ce Ta Harzuka Wanda Suka Sace Mu, Suka Fara Dukanmu -Wanda Ya Kubuta

bySadiq
3 years ago
Gwamnati

Daya daga cikin fasinjojin jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna, mai suna Hassan Usman da ya kubuta da yammacin yau Litinin, ya ce gwamnati ce ta harzuka ‘yan ta’addan suka fara gana musu azaba.

Usman ya kubuta tare da wasu mutane biyu; mace daya da namiji daya.

  • ‘Yan Ta’adda Sun Kai Wa Sojoji Hari A Abuja
  • Jami’an Tsaro Sun Kashe Mahara 2 A Anambra, Sun Kwato Makamai 

A tattaunawarsa da BBC Hausa, ya bayyana irin halin da ya tsinci kansa tare sa sauran wadanda ‘yan ta’addan suka sace a lokacin harin jirgin kasan.

“Da farko a waje muke kwana a kasan bishiya, amma da aka fara ruwan sama sun yi mana rumfa da shimfidu da muke kwana a kai.”

Ta fuskar abinci kuwa, ya bayyana cewar ‘yan bindigar sun yi kokari iyakarsu wajen ganin sun ba su cima mai kyau.

“Eh to abinci alhamdulilah suna iya kokarinsu gaskiya, suna ba mu abinci daidai karfinsu a wani lokaci ma har yanka suke mana na shanu da awakai.

“Akalla ko jiya (Lahadi) sun yanka mana sa mun ci alhamdulilah,” in ji shi.

Sai dai kuma ya ce gwamnatin tarayya ta fusata ‘yan ta’addan wanda hakan ya sa suka fara dukansu, kuma sun shirya gana musu azaba iri-iri.

“Eh to tun da muka je, gwamnati ce ta harzuka su har suka fara daukar matakai na duka kamar yadda kuka gani a bidiyon da aka sani, mun sha duka matukar duka.

“Kuma wannan ma somin tabi ne saboda har yanzu ‘yan uwana ina jimamin cikin yanayin da zasu sake shiga idan ba a kawo musu dauki ba, shi yasa wannan bidiyon ya fito.

“Shi yasa muka yi kira ga wasu kasashen tun da muna ganin mu gwamnatinmu ta Nijeriya ta gaza har muka zauna wajen wata hudu,” in ji shi.

A karshen mako ne dai ‘yan ta’addan suka saki wani sabon bidiyo suna dukan fasinjojin da suka yi garkuwa da su.

Hakan ya harzuka ‘yan Nijeriya da dama, inda kowa ke ganin gwamnatin tarayya gaza samar da tsaron da take ta ikirari.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taron Dandalin Tattaunawar Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka Karo Na Biyu

Xi Ya Aike Da Sakon Taya Murna Ga Taron Dandalin Tattaunawar Zaman Lafiya Da Tsaro Na Sin Da Afirka Karo Na Biyu

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version