• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Gombe Ta Bukaci Jami’an Lafiya Da Su Kara Kwazo Wajen Yaki Da Cutar Sida

by Yunusa Isa
2 years ago
Gombe

Gwamnatin Jihar Gombe ta umarci Ma’aikatar Lafiya ta jihar da hukumar yaƙi da cutar sida ta jihar (GOMSACA) da kuma hukumar kula da lafiya a matakin farko ta Jihar da su samar da dabarun ɗorewar nasarorin da aka samu a yaƙi da cutar ta Sida a jihar.

Sakataren Gwamnatin Jihar, Farfesa Ibrahim Abubakar Njoɗi, ne ya bayar da wannan umarnin yayin da ya karɓi baƙuncin babbar tawagar yaƙi da cutar Sida ta Jihar Gombe (GOMSACA) bisa rakiyar Hukumar Yaki da Cutar Sida ta ƙasa (NACA), da Cibiyar Kula da Shirye-shiryen Kiwon Lafiya (CIHP) tare da sauran masu ruwa da tsaki da kuma abokan hulɗa a wata ziyarar da suka kai a gidan gwamnati.

  • Sallah: Yadda Sarkin Gombe Ya Jagoranci Hawan Daba
  • Hutun Haihuwa: An Samu Masu Yin Tazara 28,561 A Farkon 2023 A Jihar Gombe

Sakataren ya ce; cutar Sida wata abar damuwa ce ga gwamnatin jihar, yana mai bada tabbacin cewa za ta yi duk mai yiwuwa don daƙile yaduwarta a jihar.

Da yake yabawa tawagar bisa jajircewarta na rage illar cutar a jihar, Farfesa Njoɗi, ya bayar da tabbacin cewa gwamnatin jihar zata tabbatar da ɗorewar yaƙin da tabbatar da nasarorin da aka samu ta hanyar jajircewa da gudummawar da abokanan hulɗar ci gaba suka bayar.

“Mun fahimci damuwar ku game da ɗorewar wannan shiri, ba za mu ci gaba da zama mabarata ba; muna jiran tallafi daga abokan hulɗar ci gaba a ko da yaushe, kowa yana ƙoƙari ya bayar da ta shi gudummawa a duniya, dole ne muma mu yi iya bakin ƙoƙarinmu wajen yiwa jama’a hidima”.

Don haka sakataren ya umurci ma’aikatar lafiya da hukumomin da abin ya shafa da su samar da hanyoyin da za a ci gaba da yaki da cutar da ɗabbaƙa nasarorin da aka samu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin
Manyan Labarai

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Next Post
Za A Sake Gurfanar Da Faston Da Ake Zargi Da Sa Mabiyansa Azumin Mutuwa

‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Yi Wa Jama’a Kutse A Asusun Banki

LABARAI MASU NASABA

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

Gobara Ta Sake Ƙone Kasuwar Oba A Benin

October 9, 2025
Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version