Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Gwamnatin Jihar Nasarawa Ta Kaddamar Da Takin Zamani Kan Naira 5,000

by Muhammad
January 21, 2021
in RIGAR 'YANCI
3 min read
Takin Zaman
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Zubairu M Lawal,

Gwamnan jihar Nasarawa Injiniya Abdullah Sule ya kaddamar da takin zamani tare da kayan amfanin gona kan farashi mai rahusa.

samndaads

Gwamnan ya ce duk da cewa muna lokacin ranine amma babban burinmu jihar mu ta zamo kan gaba wajen fitar da abinci a lokacin rani da damuna.

Gwamna Abdullah Sule ya gargadi jami’an kula da rarraba takin zamanin da su tabbatar da cewa wadannan kayayakin sun shiga hannun manoma kuma ’yan jihar.

Gwamna Abdullah Sule ya gargadi jami’an kula da wannan kayan kada su sake a maimaita irin abin da ya faru a shekarar baya.

Ya nanata cewa gwamnatinsa na son tabbatar da cewa duk abin da za a rarraba, ya kamata ya tafi kai tsaye ga masu amfani da shi, ba tare da wani ya tsoma baki kan aikin ba.

A cewar Injiniya Sule, idan takin da sauran abubuwan suka kasa kaiwa ga wadanda ake so din a shekarar da ta gabata, ya kamata jami’an da ke kula da rabon ya bullo da sabuwar dabara don tabbatar da kayayyakin sun isa ga manoman.

Gwamnan ya bayyana cewa gwamnati ta tallafa da takin kuma za a sayar wa manoma kan Naira 5,000 a kowace buhu.

Ya ce biyo bayan alkawarin da gwamnatinsa ta dauka a farko don inganta bangaren noma don ci gaban tattalin arziki na jihar, Gwamnati ta ci gaba da ba wa bangaren kaso mafi girma a aikin gona. Saboda shi ne babbar sana’ar kusan kashi 80 na al’ummar jihar.

Gwamnan ya ce, “Wannan an yi shi ne domin inganta rayuwar mutanenmu, don tabbatar da samar da aiyukan yi mai tsoka ga ma’aikata, tare da samar da wadataccen abinci a jiharmu.”

Injiniya Sule ya yi nuni da cewa saboda jihar Nasarawa tana da kasa mai kyau da kuma yanayi mai kyau wanda ya dace da noman amfanin gona don amfanin gida da kuma fitar da shi kasa shen waje. Ya kara da cewa Gwamnatin sa ta yi amfani da damar don jawo hankalin masu saka jari zuwa jihar.

Haka nan, Rukunin Dangote, wanda ke mamaye fili mai girman hekta 68, 000, da nufin samar da sukari sama da metric tan 420,000, wanda ya kai kashi 35 na yawan sukarin da ake amfani da shi a kasar.

Shinkafar Azman, wacce ke da hecta sama da 14,000 a karamar hukumar Toto, tana aikin samar da shinkafa a yankin, da kuma Fulawar Mills na Nijeriya, wacce ta samu kadada 20, 000 kuma a karamar hukumar Toto, ta amfani hekta 10,000 don noman rake da kuma hekta dubu 10, don noman rogo.

Gwamnan ya ci gaba da bayyana cewa Gwamnatin sa ta ci gaba da yin hadin gwiwa da kungiyoyi daban-daban, wadanda suka ga Gwamnatin jihar ta jajirce wajen siyan wasu kayayyakin aikin gona na zamani da za su taimaka wa manoma wajen kiyaye amfanin gonarsu.

Wannan hadin gwiwar, a cewar Injiniya Sule ya jawo hankalin wani kamfanin kasar Jamus mai aikin gona wanda ba zai iya kerawa da kuma hada kayan aikin noma a jihar Nasarawa ba, tare da karin kudurin sayan wadannan kayan aikin da suka kai 250 ga manoman jihar.

A nasa jawabin, Ministan harkan Noma da Raya Karkara, Alhaji Sabo Nanono, wanda ya samu wakilcin Hajiya Karima Babangida, wata darakta a ma’aikatar, ya yaba wa Gwamnatin Jihar Nasarawa kan fara rabon takin zamani da sauran kayan aikin gona don noman rani na shekarar 2020/21, wanda zai dore har tsawon shekara. zagaye noma.

Ministan ya yi tir da cewa tsarin samar da abinci a kasar na fuskantar kalubale sakamakon tasirin canjin yanayi, wadanda suka hada da bala’in ambaliyar ruwa a yankunan Arewa da Tsakiyar kasar, rashin kyakkyawan ruwan sama a Kudanci da kuma annobar Korona.

Alhaji Nanono ya bayyana cewa an zabi jihar Nasarawa ne cikin jihohi 9 da za su ci gajiyar shirin shiga tsakani na ma’aikatar saboda tana daga cikin kwandunan abinci na kasar.

Hajiya Karima Babangida ta mika tallafin Kayayyakin da ma’aikatar ta bayar da suka hada da buhu 200 na ingantaccen irin shinkafa, lita 1,000 na maganin kashe ciyawa, lita 800 na maganin kwari, buhu 800 na takin NPK, buhu 400 na takin Urea da kuma lita 800 na gyaran kasa.

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnan Jihar Nasarawa Ya Bayyana Damuwarsa Kan Biyan Albashin Ma’aikata

Next Post

Hadimar Gwamna Ta Yi Murabus Domin Da Tsira Da Aurenta

RelatedPosts

Ummu-Kalthum Sambo

Tallan ’Ya’ya Mata Kalubale Ne Babba – Ummu-Kalthum Sambo

by Sulaiman Ibrahim
20 hours ago
0

Daga Idris Umar,Zariya   A cikin makon daya gabacemu ne...

Ihiya'ussuna

Makarantar Ihiya’ussuna Ta Yi Sauka Karo Na Tara

by Sulaiman Ibrahim
20 hours ago
0

Daga Idris Umar Zariya   Madarasatu ihiya'ussuna school of Arabic...

NARICT

NARICT: ’Yan Kungiyoyi Sun Yaba Wa Cigaban Da Farfesa Barminas Ke Samarwa A Zariya

by Sulaiman Ibrahim
20 hours ago
0

Daga Idris Umar, Zariya   Mambobin kungiyoyin al'umma da ke...

Next Post
Hadimar

Hadimar Gwamna Ta Yi Murabus Domin Da Tsira Da Aurenta

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version