Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RAHOTANNI

Gwamnatin Kaduna Ta Kaddamar Da Aikin Hanya A Kauru

by Tayo Adelaja
September 15, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Ibrahim Ibrahim,  Kaduna

Gwamnatin Jihar Kaduna a karkashin jagorancin Malam Nasiru Ahmed El- rufai, a cikin shirinta na raya karkara da al’umma ta kaddamar da hanya mai tsawon kilo mita goma  12  wadda ta tashi daga Barwa  ta shiga Zakada zuwa Bandi Amawa da ke Karamar Hukumar Kauru.

A Jawabinta yayin  kaddamar da hanyar, Kwamishinar ma’aikatar raya karkara da al’umma ta jihar  Hajiya Balaraba ta ce,   wannan hanyar ita ce ta farko da ma’aikatarta ta fara kaddamarwa a cikin shekara daya  da su kayi a ofis, Ta bakinta, “Hakika yau ranar farin ciki ne a gare ni kasancewar wannan hanyar ita ce irin  ta na farko da ma’aikatarnmu za ta fara kaddamarwa  a cikin shekara daya da mukayi a ofis. Haka kuma yau ranar farin ciki ne a gare ni, domin ta kassance ranar da muka cika alkawarin da gwamnatin Malam  Nasiru Ahmed El-rufai ta dauka na inganta rayuwar  al’ ummar karkara.”

Hajiya  Balaraba ta ci gaba da cewa, hanyar mai tsawon kilo mita goma sha biyu wacce aka yi ta a kan kudi naira miliyan dari da casa’in da bakwai, daya ce daga cikin hanyoyi tara da ma’aikatar ta yi wanda za ta kaddamar da sauran nan ba da dadewa ba.

“Kamar yadda kuka sani, gwamnatin Jihar Kaduna a karkashin jagorancin Malam  Nasiru Ahmed El-rufai, kokarinta a kullum shi ne ta ga  yadda za ta kyautata wa rayuwar al’ummar jihar nan musamman mazauna yankin karkara”, in Kwamishinar.

Ta ci gaba da cewa, “Gwamna ya fahimci cewa mafi yawancin mutanen jihar suna zaune ne a yankunan karkara, don haka ne ya mayar da hankalinsa wajen wadata su da hanyoyi, da kuma gyara asibitoci, makarantu, samar da wutar lantarki da ruwan sha mai tsabta. An sake dawo da ma’aikatar raya karkara da jin dadin al’umma ta wannan jihar a shekarar da ta gabata don tabbatar da an kawar da talauci, kuma al ummar karkara sun zama masu wadata da mutunci,  don haka yin hanyoyi yakan saukaka fitowa da amfanin gona, karfafa kasuwanci, sada zumunci, da sauran harkokin rayuwa na yau da kullum kamar zuwa makarantu da asibitoci a cikin sauki”.

Bugu da kari, Hajiya Balaraba ta ce,  Gwamnatin Malam  Nasiru ta kafa kwamiti mai karfi domin duba duk muhimman abubuwan bukatun da jama’ar Karamar Hukumar Kauru ke da su don basu tallafin gaggawa.

A karshe, ta shawarce su da su yi kokarin  kafa kugiyoyin ayyukan gayya domin ta haka ne kadai za su samu damar hadin kan da zai ba su damar cin moriyar  dimokuradiyyan da muke ciki.

A jawabinsa na godiya, Aliyu Dahiru wanda shi ne  Sarkin Garin Zakada, ya jinjina wa gwamnatin Malam Nasiru Elrufai bisa hanyar da ta samar musu. A cewarsa, “Mu kadai muka san wahalar da muke sha idan za mu shiga garuruwan da muke makwabtaka da su, amma yanzu an share mana hawaye, sai dai muna kara rokon mai girma gwamna da ya zo ya yi mana kwalta domin mu dade muna cin moriyar hanyar, sannan kuma muna baukatar a kara turo mana da  abubuwan more rayuwa”.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

An Bukaci ‘Yan Kasuwa Su Sassauta Farashin Kayayyaki

Next Post

NANS Ta Yi Kira Ga Gwamnati Da Kungiyar Malamai Kan Yajin Aikin Jami’o’i

RelatedPosts

Amin

Yadda Ta Kaya A Taron Tunawa Da Malam Aminu Kano Karo Na 19

by Muhammad
2 mins ago
0

Mun Gamsu Da Yadda Aka Tsara Taron Kan Tsaro Da...

AKCOE

Mataimakin Shugaba Kwalejin AKCOE Ya Zama Jakadan Zaman Lafiya A Nijeriya

by Muhammad
27 mins ago
0

Daga Mustapha Ibrahim, Mataimakin Shugaban Kwalijin Ilimi ta Aminu Kano...

Allah

An Roki Al’umma Su Dogara Ga Allah  

by Muhammad
45 mins ago
0

Daga Yusuf Abdullahi Yakasai, Alhaji Bello Otunba wanda yake daya...

Next Post

NANS Ta Yi Kira Ga Gwamnati Da Kungiyar Malamai Kan Yajin Aikin Jami’o’i

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version