Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Gwamnatin Kebbi Ta Raba Wa Fulani  2,778 Tallafin  Dabbobi

by Muhammad
December 27, 2020
in LABARAI
3 min read
Dabbobi
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Umar Faruk Birnin-Kebbi,

Gwamnatin jihar Kebbi a jiya ta baiwa al’ummar Fulani 2,778 tallafin Dabbobin da kuma abinci domin inganta rayuwar su a duk fadin jihar ta Kebbi.

samndaads

An kaddamar da bikin bada tallafin ne a rugar Hulkui da ke a cikin karamar hukumar Mulki ta Maiyama a jihar ta Kebbi a jiya, inda Fulanin yankin na karamar hukumar mulki ta Maiyama sun samu tallafin Tumaki da raguna da kuma abincinsu, haka kuma wasu sun samu shanun yin madara da abin da kuma kudi Naira dubu arba’in da kuma wayar hannu domin a rika sanin yanayin da  dabbobin da aka basu suke ciki.

Dabbobin da aka bayar a wurin taron bikin sun hada da Tumaki, Awaki, Kaji da kuma Shanu, Sai  abincin dabbobi da kuma kaddamar da tsarin yin madara ga Matan Fulani makiyaya wato (Yoghurt)  har da kuma tsarin karbar madarar da za su samar ga hannun matan na Fulani makiyaya .

Tallafin dai wata hanya ce da gwamnatin jihar Kebbi ta  fito da ita  a matsayin wani shiri na bada tallafin na bashi ga al’ummar Fulani makiyaya domin karfafawa da kuma inganta rayuwar Fulani makiyaya na jihar a karkashin jagorancin Gwamna Abubakar Atiku Bagudu tare hadin gwiwar ma’aikatar kula da dabbobi da kuma kiwon kifi ta jihar ta taimakon kungiyar Fulani wato Miyelti-Allah  reshen jihar ta Kebbi domin tabbatar da cewa Fulani makiyaya a jihar sun kara samun sana’o’in da za su dogaro da kansu, wanda hakan wata dama ce ta a de na yi wa  al’ummar Fulani kallon ‘yan ta’adda  ko masu hannu daga cikin aikata miyagun laifufuka a jihohin kasar nan.

Da yake jawabi a wurin taron bikin kaddamar da bada tallafin dabbobi ga Fulani makiyaya na karamar hukumar Mulki ta Maiyama,  Kwamishinan ma’aikatar Kula da dabbobi da kiwon kifi, Aminu Garba Dandiga  ya bayyana cewa” gwamnatin jihar Kebbi a karkashin jagorancin Gwamna Abubakar Atiku Bagudu, a matsayina na Kwamishinan ma’aikatar  Dabbobi akwai tsari guda bakwai da aka fito dashi wanda na bada tallafi ga Fulani makiyaya na duk fadin jihar, bisa ga hakan ne zamu kaddamar da tsarin

guda daya  a wannan karamar hukumar ta Maiyama wanda rugar Hulkui ne za a kaddamar da tsarin kuma su ne zasu ci gajiyar tsarin da gwamnatin jihar Kebbi ta fito dashi, inji Kwamishinan ma’aikatar Dabbobi da kiwon kifi Alhaji Aminu Garba Dandiga yayin gabatar da jawabinsa”.

Haka kuma ya ci gaba da cewa” duk mutunen  da ke  cikin tsarin kiwon Tumaki, kowane mutun guda za a bashi Tunkiya biyu da rago da kuma abincinsu domin yayi kiyo ido suka haihu za a karba a ba na kusa gare shi domin shi ma ya ci gajiyar. Sai kuma mutanen da ke cikin tsarin kiwon Awaki da Kaji suma tsarin su daya ne. Amma masu  samar da madarar Yoghurt za su raba riba ne gida biyu sai su bada kashi daya su kuma su amfana da kashi daya, inji shi”.

Haka kuma wakilinmu ya samu jin ta bakin daya daga cikin matan fulani makiyaya da ta samu nasarar ci gajiyar tsarin maisuna Aisha Muhammad ta ce” muna godiya ga gwamnatin jihar Kebbi a karkashin jagorancin Gwamna Abubakar Atiku Bagudu da kuma Kwamishinan ma’aikatar Dabbobin Alhaji Aminu Garba Dandiga kan irin wannan tallafi da aka basu. Ta kuma bada tabbacin cewa zasu yi amfani da wannan tallafi da aka basu domin kara inganta rayuwar su ta hanyar yin sana’ar kiwon Tumaki da kuma kaji, inji Aisha Muhammad da ke a rugar Hulkui ta garin Maiyama”.

SendShareTweetShare
Previous Post

Tarbiyar Da Mahaifimmu Ya Bamu Ita Take Mana Kyakkyawan Jagoranci -Kwankwaso

Next Post

Jihar Kaduna Ta Ware Naira Biliyan 4.6 Don Daga Darajar Asibitoci

RelatedPosts

Zaben Dan Majalisa

Za A yi Zaɓen Gwamnan Anambara Ranar 6 Ga Nuwamba – INEC

by Sulaiman Ibrahim
1 hour ago
0

HUKUMAR Zaɓe ta Ƙasa (INEC) ta bayyana cewa a ranar...

Ogun

Fashewar Tankar Mai Ya Ci Rayuwar Mutum Uku Da Jittaka Shida A Ogun

by Muhammad
8 hours ago
0

Daga Khalid Idris Doya, A ranar Talata ne mutum uku...

Bafarawa

’Yan Nijeriya Sun Fi So A Magance Rashin Tsaro Fiye Da Korona, Cewar Bafarawa

by Muhammad
8 hours ago
0

A Juya Kuɗin Rigakafin Cutar Naira Biliyan 400 Zuwa Tsaro...

Next Post
Darajar

Jihar Kaduna Ta Ware Naira Biliyan 4.6 Don Daga Darajar Asibitoci

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version