Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RAHOTANNI

Gwamnatin Nasarawa Za Hada Gwiwa Da Turai Kan Bunkasa Tattalin arziki

by Tayo Adelaja
September 22, 2017
in RAHOTANNI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Abubakar Abdullahi, lafia

A kokarin da take na samar da aikin yi da kuma bunkasa tatalin arzikin jihar, gwamnatin Jihar Nasarawa a karkashin jagorancin Gwamna Umaru Tanko Al-Makura, tana lalubo hanyoyin hadin gwiwa da wasu kasashen Turai su hudu da suka hada da Sweden, Finland, Denmark da kuma Norway don cimma kudurinta.

Gwamnan jihar Umaru Tanko Al-Makura ya sanar da haka a yayin da ya karbi bakuncin jakadun kasashen hudu a fadar gwamnati da ke Lafia cikin wannan mako.

Gwamnan wanda ya bayyana jin dadinsa kan ziyarar, ya ce kasashen sun kasance a jerin kasashen duniya masu karfafa zaman lafiya a duniya, suna kuma bada gudunmawa a bangarori daban-daban da suka hada da fannin noma da kiwon lafiya da ilimi da gine-ginen, da wannan ya ce zai zama alfanu ga jihar ta yi hadin gwiwa da su.

Al-Makura ya ce, “Daga cikin kasashen, kasa kamar Sweden ta taimaka wa jihar wajen tsara ayyukan hukumar ajiyar bayanan filaye cikin na’urar kwamfuta ta jihar wanda hakan ya kawo cigaba mai yawan gaske a fadin jihar”.

Don haka ya ce gwamnati za ta so kasashen hudu su hada kai da gwamnatin jihar wajen tafiyar da harkokin sabuwar makarantar nakasassu da gwamnatin ta gina, tare da cewa ana sa ran makarantar za ta soma aiki a farkon shekara mai zuwa.

Da suke jawabi, jakadun kasashen Sweden Inger Ultbedt da na Finland Pirjo Suomela Chowhury da Norway Jens Peter Ktempruel da kuma na Denmark Torben Gettermann, duk sun yaba da irin karbar da suka samu. Suna masu cewa, ziyarar tasu ta ba su damar ganin irin abubuwan da jihar ke da su kuma idan sun hada kai da jihar za a ci riba sosai.  Duka jawaban bakin sun fi karkata ne zuwa ga fannin noma, inda suka ce hakan zai samar da abinci da kuma sana’o’i ga matasa.

Tun farko a nasa jawabin, jakadan Nijeriya a kasar Sweden wanda dan asalin Jihar  Nasarawa ne, Musa Ilu Mohammed, wanda kuma bisa gayyatarsa ce jakadun hudu suka ziyarci jihar, ya ce ziyarar takwarorin nasa ya ba su damar kara sanin Nijeriya da kuma nuna musu irin gudunmawar da za su kara bai wa kasa. Tare da cewa zai yi aiki kafada da kafada da takwarorin nasa domin kawo cigaba ga daukacin kasashen.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Gwamnatin Kano Ta Jaddada Dokar Hana Goyo A Babur

Next Post

Rayuwata A Shekara 90 Da Haihuwa — Shaikh Dahiru Bauchi

RelatedPosts

Kayan Marmari

Gwamnatin Jihar Katsina Ta Yi Gyara A Kan Tsarin Makarantun Islamiyya

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Daga Sagir Abubakar Katsina Majalissar zartarwa ta Jihar Katsina ta...

Korar Ma’aikata A Kaduna Ta Kara Jefa Jama’a Mawuyacin Hali – Isah Ashiru

Korar Ma’aikata A Kaduna Ta Kara Jefa Jama’a Mawuyacin Hali – Isah Ashiru

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Daga Abubakar Abba, Kaduna Dan takarar Gwamnan Jihar Kaduna karkashin...

Babandede Ya Yi Gargadi A Kan Daukan Aiki Na Bogi Da Sunan NIS

Sauye-sauye Masu Ma’ana A Sashen Fasfo Na Hukumar Shige Da Ficen Nijeriya

by Yahuzajere
3 days ago
0

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya (NIS), karkashin...

Next Post

Rayuwata A Shekara 90 Da Haihuwa — Shaikh Dahiru Bauchi

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version