Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
ADVERTISEMENT
Home RAHOTANNI

Gwamnatin Neja Za Ta Canja Fasalin Matsugunnai A Minna

by Muhammad
April 6, 2021
in RAHOTANNI
2 min read
Neja
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Muhammad Awwal Umar,

Gwamnan Neja, Abubakar Sani Bello ya bayyana cewar Barikin Sale, Kpakungu da wasu unguwanni na zama tamkar wasu yankuna mafi hadari wanda wajibi ne a dauki matakin gaggawa dan duba yanayin tsarin unguwanni dan canja masu fasali.

Gwamnan yace akwai tsari marar inganci da kuma rashin sanya idanu daga ma’aikatu da hukumomin da ke da alhakin kula da cigaban tsarin unguwanni tsawon shekaru da dama, wanda a cewarsa gwamnatinsa za ta yi dubi dan yin gyare gyaren kurakuran da aka yi.

“Akwai kurakurai da aka tafka a baya, kuma ya kamata mu fara gyare gyaren nan yanzu. Koda kuwa zai dauke mu kashe kudade masu yawa, za mu canja fasalin wadannan unguwannin domin mu samar masu hanyoyin da za su iya samun cigaba ta yadda jama’a zasu anfana”.

Gwamna Sani Bello, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake duba wasu ayyukan da ke gudana da wadanda aka kammala a cikin garin Minna, ya umurci hukumar kula da tsaftar muhalli ( NISEPA) da ta gaggauta tsaftace magudanan ruwa saboda fuskantar damanar bana dan kaucewa ambaliyar ruwan sama a wannan shekarar.

Gwamnan ya nuna damuwarsa akan yadda wasu unguwanni da wasu daidaikun jama’a suka mayar da magudanan ruwa wajen zuba bola, inda sau da dama duk wani yunkurin gwamnati na samu koma baya saboda rashin tsawatawa wanda a karshe kuma hakan kan jawo ambaliyar.

” Mazauna unguwannin da daidaikun jama’a ba sa taimakawa ta hanyar toshe magudanan ruwa ta hanyar zuba bola, wanda ya kamata a daina. Ba za mu jira sai lokaci ya kure ba ta hanyar share magudanan ruwan saboda ruwan sama na gab da sauka ba da jimawa ba”.

A karshen duba ayyukan hanyoyin da gwamnan yake yi, gwamna Sani Bello ya nuna gamsuwarsa da yanayin inda aikin ya kai, sai dai ya nemi ‘yan kwangilar da su kara kaimi akan yadda suke gudanar da aikin kuma su tabbatar sun kammala aikin cikin kankanin lokaci.

SendShareTweetShare
Previous Post

Fadar Shugaban Kasa Ta Caccaki Bishop Kukah Bisa Kalamansa Na Bikin Ista

Next Post

Dokajin Gaya Ya Nada Ambasada Yusuf Ibrahim Wakilin Dukiya  

RelatedPosts

Zamfara

Gwamnatin Jihar Zamfara Ta Tabbatar Da Kama  Wasu Sojoji Masu Hulda Da ‘Yan Ta’adda

by Muhammad
15 hours ago
0

Daga Hussaini Yero, Gwamnatin jihar Zamfara ta tabbatar da rahotan...

Mota

Yaki Da ‘Yan Ta’adda: Zulum Ya Ba Sojoji Gudummuwar Mota 12

by Muhammad
15 hours ago
0

Sheran jiya Juma’a ce gwamna jihar Borno Babagana Zulum, ya...

Tsangaya

Yadda Aka Fara Karatun Tsangaya A Musulunci Da Lalacewarsa A Kasar Hausa – Gwani Yahuza 

by Muhammad
15 hours ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Shugaban hukumar kula da makarantun Al’kur’ani...

Next Post
Gaya

Dokajin Gaya Ya Nada Ambasada Yusuf Ibrahim Wakilin Dukiya  

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version