Yusuf Shuaibu">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home TATTALIN ARZIKI

Gwamnatin Nijeriya Ta Ware Naira Biliyan 10 Domin Samar Da Magungunan Korona

by Yusuf Shuaibu
January 20, 2021
in TATTALIN ARZIKI
2 min read
Samar Da Allurar Rigakafin COVID-19 Cikin Adalci Zai Taimaka Wa Afirka Wajen Yakar Annobar
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Ma’aikatar kudi ta ware naira biliyan 10 domin samar da magungunar cutar Korona a kasar nan, kamar yadda hukumomi suka bayyana.

Ministan lafiya, Osagie Ehanire ya bayyana cewa, an ware naira biliyan 10 wajen sayo wa ‘yan Nijeriya magungunan Korona. Mista Ehanire ya bayyana hakan ne wajen taron manema labarai na kwamitin shugaban kasa kan cutar Korona wanda ya faru a ranar Litinin. Ya bayyana cewa, ana tsammanin samun magungunan cutar Korona guda miliyan 10 wanda za a kawo a cikin watan Maris ta shekarar 2021. Ya kara da cewa, Nijeriya ta shiga cikin tawagar kungiyar kasashe yankin Afirka masu neman magungunan cutar Korona, wanda a yanzu haka akwai ire-iren magungunar cutar Korona miliyan 270.

samndaads

“Ma’aikatar kudi ta tarayya ta ware naira biliyan 10 domin samar da magungunar cutar Korona a cikin kasar nan.

“A saka rai za a samu sami kyakkyawan muhalli da ababen more rayuwa da samun damar zuba jari da kuma samun magungunar cutar Korona huda miliyan 10, wanda za a fara rarrabawa a watan Maris ta shekarar 2021.

Ya bukaci ‘yan Nijeriya su kaucewa wadannan mutune da suke ikirarin sayar da magungunar cutar Korona a cikin kasar nan.

“Ina shawartar ‘yan kasa su yi watsi da duk wani ikirarin wasu ‘yan ta’adda. Za a samar da magunguna wadanda za a yi amfani da su wanda ya samu amincewar hukumar kula da ingancin abinci da kuma magunguna ta kasa (NAFDAC).

“Ina shawartar mutane su kula da jabun magunguna, amma a yanzu babu wani magani da kasar nan ta amince da shi. Hukumar bunkasa lafiya matakin farko (NPHCDA) ita ce hukumar da za a amince da duk wani magani a cikin kasar nan,” in ji shi.

Gwamnatin tarayya Nijeriya ta bayyana cewa, za a sami magunguna huda 100,000 na kashe cutar Korona kafin karshen watan Junairun shekarar 2021, wanda za a tabbatar kowani dan kasa ya samu kariya daga cutar Korona. Haka kuma ta bayyana cewa, ana tsammanin kasar za ta iya samun karin magungunan guda miliyan 42 daga baya.

Mista Ehanire ya ci gaba da cewa, ana ci gaba da samun sababbin mutane masu dauke da cutar a cikin kasar nan, wanda an tabbatar da mutane 10,300 suke dauke da cutar, sannan an guda mutum 50,750 a cikin mako guda daya, wannan ne ke nuna an samu karuwar kashi 20. Ya ce, a duk kullum sai an gwada mutum biyan har zuwa tsawan mako guda wadanda suke dauke da cutar, an samu karuwar kashi 14 idan aka kwatanta da na makonnin baya.

“Jimillar masu dauke da cutar a Nijeriya wadanda aka tabbatar sun kai 110,387 a cikin mutane 1,172,234 wanda aka gwada, wanda ya kai na kashi 9.4. An samu mutum 1,444 wadanda suka kamu da cutar a cikin awanni 24, an kuma samu mutum 77 da suka mutu a makon da ta gabatar wanda yah ade jimillar mutanen da suka mutu sun kai 1,435.

“An samu mutane wadanda suka kai kashi 20 wadanda aka tabbatar da sun kamu da a watar Junairu fiye wanda aka samu a watan Disamba,” in ji shi.

 

SendShareTweetShare
Previous Post

CBN Ta Bada Tallafin Biliyan N10 Domin Farfado Da Kamfanoni A Kano

Next Post

FIRS Ta Tattara Harajin Tiriliyan N4.9 A Shekarar 2020 Duk Da Korona

RelatedPosts

Farashin Dizel Ya Yi Tashin Gwauron Zabi

Farashin Dizel Ya Yi Tashin Gwauron Zabi

by Yusuf Shuaibu
1 day ago
0

Farashin dizil ya yi tashin gwauron zabi wanda lita daya...

Korona Ta Kawo Tsaikon Kammala Matatar Man Dangote Zuwa 2021

Matatun Man Dangote Za Su karfafa Darajar Naira Da Ceto Tattalin Arziki – Majalisar Wakilai

by Yusuf Shuaibu
1 day ago
0

Majalisar Wakilan Nijeriya ta bayyana cewa, matatan man kamfanin Dangote...

“Duk Da An Sauya Shugabannin Tsaro, Har Yanzu Da Saura”

Na Shirya Tsaf Don Fitar Da Mutum Miliyan 100 Daga Kangin Talauci – Shugaba Buhari

by Yusuf Shuaibu
1 day ago
0

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa, burin gwamnatinsa na...

Next Post
FIRS

FIRS Ta Tattara Harajin Tiriliyan N4.9 A Shekarar 2020 Duk Da Korona

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version