Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home MANYAN LABARAI

Gwamnatin Sakkwato Ta Mayar Da Makarantun Allo 4,000 Zuwa Na Zamani

by Tayo Adelaja
September 12, 2017
in MANYAN LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto

Gwamnatin Jihar Sakkwato ta mayar da makarantun Kur’ani dubu hudu zuwa makarantun ilimin zamani domin kara adadin yawan dalibai masu shiga makarantun furamare.

samndaads

Kwamishinan Ma’aikatar Ilimin Firamare da na Sakandare, Dakta Muhammad Jabbi Kilgori ne ya bayyana hakan a ranar Lahadi a yayin da yake ziyarar duba daya daga cikin makarantun a garin Takatuku da ke Karamar Hukumar Bodinga.

Ya ce an riga an kaddamar da kwamitin Sarakunan Gargajiya a karkashin jagorancin Mai Alfarma Sarkin Musulmi Muhammadu Sa’ad Abubakar kan wannan shirin.

Kilgori ya bayyana cewar shirin agajin gaggawa da Gwamnatin Sakkwato ta kafa yana haifar da da mai ido ta hanyar gine- gine, samar da malamai da sauran agaji da dama.

Ya ce an tura malamai a makarantu a garuruwan da suke zaune domin su magance matsalar rashin zuwa aiki.

Kwamishinan ya kara da cewar Gwamnati ta samar da gine-ginen da za a fadada zababbun makarantun wadanda za su bayar da ilimin addinin Musulunci da darussan ilimin zamani a hade.

Tun da fari, Shugaban Makarantar, Sa’idu Nata’ala ya bayyana cewar makarantar ta na da dalibai 64  wadanda shekarun su suka kama tsakanin shida zuwa 12 wadanda ke karbar ilimin Kur’ani da na zamani.

Daga nan ya bayyanawa Kwamishinan cewar UNICEF ta bayar kayan aiki ga makarantar domin tallafawa shirin. Haka ma Shugaban Makarantar ya yi korafin rashin wadataccen muhallin da za a fadada makarantar domin a cewarsa suna bukatar karin gine-gine da kayan aiki.

 

 

SendShareTweetShare
Previous Post

Nadal Ya Lashe Kofin Gasar Tennis Na Us Open Karo Na 3

Next Post

Daga Rohingya Zuwa Sambisa: Me Muka Rasa A Mutun-taka?

RelatedPosts

Shugabannin Tsaro

Me Saukar Shugabannin Tsaron Nijeriya Ke Nufi?

by Muhammad
17 hours ago
0

Sauka Suka Yi Don Kashin Kansu – Fadar Shugaban Kasa...

Zakzaky

Korona: Ku Mika Matar Sheikh El-Zakzaky Cibiyar Killacewa

by Muhammad
2 days ago
0

–Umarnin Kotu Ga Gidan Yarin Kaduna Daga Rabiu Ali Indabawa,...

Rigakafi

Korona: Jiga-jigan Nijeriya Na Sulale Wa Waje Amsar Rigakafi

by Muhammad
3 days ago
0

Daga Khalid Idris Doya, Biyo bayan sake bullar annobar Korona...

Next Post

Daga Rohingya Zuwa Sambisa: Me Muka Rasa A Mutun-taka?

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version