Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RAHOTANNI

Gwamnatin Sakkwato Za Ta Sayar Da Gidajen Gwamnati 1,500

by Tayo Adelaja
September 14, 2017
in RAHOTANNI
1 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Sharfaddeen Sidi Umar, Sokoto

Domin baiwa ma’aikata damar mallakar muhalli na kashin kansu, kwamitin da Gwamnatin Jihar Sakkwato ta kafa kan sayar da gidajen Gwamnati ya bayar da shawarar sayar da gidaje 1500 a wurare da dama a fadin jiha.

samndaads

Shugaban kwamitin kuma Kwamishinan Filaye da Gidaje, Bello Abubakar ne ya bayyana hakan a yayin da yake mika rahoton kwamitin ga Gwamna Tambuwal.

“Kamar yadda binciken mu ya nuna akwai gidaje 1, 497 mallakar Gwamnatin Jiha a unguwanni daban-daban da suka hada da Guiwa, Bado, Arkilla Nasarawa, Runjin Sambo, GRA ta Gabas da ta Yamma.” A cewar shugaban kwamitin.

Abubakar ya bayyana cewar kwamitin ya baiwa Gwamnati shawarar wadanda za su amfana da sayen gidajen su kasance ‘yan asalin jiha wadanda ke aiki a jiha ko Kananan Hukumomi.

Ya kuma ce za a bayar da kulawar musamman ga’ ‘yan asalin jiha da ke aiki a Gwamnatin Tarayya da kuma wadanda ba ‘yan jiha ba da ke aiki da Gwamnatin jiha.

Da yake bayani bayan ya karbi rahoton kwamitin, Gwamna Tambuwal ya bayyana cewar Gwamnati ta tsara amfani da kudaden da aka samu bayan sayar da gidajen wajen kammala sababbin rukunin gidaje da Gwamnatinsa ke ginawa a cikin Birnin Jiha.

“Na gode da kwazon da kuka nuna a wannan aikin. Majalisar Zartaswar Jiha za ta zauna ta tattauna kan rahoton domin amincewa.” Inji Gwamnan.

SendShareTweetShare
Previous Post

Hajjin Bana: Likitoci Sun Duba Alhazan Jigawa 2,300 A Saudiyya

Next Post

Yadda Wani Darakta Ya Kashe Kansa A Legas

RelatedPosts

Alaba

‘Yan Kasuwan Arewa A Legas Mu Hada Kai Don Cigaba – Muhammadu Alaba

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Yusuf Abdullahi Yakasai, Hadin kai shi wani babban al’amari...

Jama'a

Taimaka Wa Jama’a Shi Ne Shugabanci Nagari -Matawalle Alagwadun Legas  

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Yusuf Abdullahi Yakasai,   Matawallen Alagbado, Alhaji Muhammadu ya...

Samarun

Yadda Rasuwar Matashi Ta Jefa Mutane Cikin Alhini A Samarun Zariya

by Muhammad
2 days ago
0

Daga Idris Umar, A ranar laraba ta wannan makon da...

Next Post

Yadda Wani Darakta Ya Kashe Kansa A Legas

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version