Nasir S Gwangwazo">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Gwamnatin Tarayya Kara Wa’adin Lambar Rijistar ’Yan Kasa Kafin Toshe Layukan Waya

by Nasir S Gwangwazo
December 22, 2020
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Gwamnatin Tarayyar Nijeriya ta kara wa’adin hade rijistar layukan waya da Lambar ’Yan Kasa zuwa watan Fabrairu na 2021 maimakon karshen wannan wata na Disamba, 2020.

Bayanin hakan ya na kunshe ne cikin wata sanarwar Ma’aikatar Sadarwa mai dauke da sa hannun hadin gwiwa tsakanin Mataimakin Shugaban Hukumar Kula da Kamfanonin Sadarwa ta Kasa (NCC) mai Cikakken Iko, Farfesa Umar Danbatta da Darakta Janar na Hukumar Kula da Katin Rijistar ’Yan Kasa (NIMC), Alhaji Aliyu Aziz a jiya Litinin.

samndaads

Sanarwar ta ce, “Kwamitin Musamman kan Tilasta Amfani da Lambar ’Yan Kasa da na Kula da Rijistar Layuka sun gana a yau (wato jiya Litinin), 21 ga Disamba, 2020

“Ministan Sadarwa, Isa Ali Pantami ne ya jagoranci ganawar, wacce ta kunshi manyan masu ruwa da tsaki na harkae da su ka hada da na hukumomin – NCC, EBC-NCC, DG-NITDA, DG-NIMC, ECTS/ECSM-NCC, Shugaban ALTON, Shugabannin MTN, Airtel, Ntel, Glo, Smile da 9Moble a wajen zaman.”

“An kara wa’adin makonni uku ga masu amfani da layuka da ke da Lambar ’Yan Kasa (NIN) su yi rijista daga 30 ga Disamba, 2020 zuwa karin 19 ga Janairu, 2021.

“An kara makonni shida ga masu layukan da ba su da NIN daga 30 ga Disamba, 2020 zuwa 9 ga Fabrairu, 2021.”

Haka nan, sanarwar ta ce, hukumar NIMC ta yi tanadin kiyaye ka’idojin kula da kamuwa da cutar Korona a lokacin rijistar.

Idan dai za a iya tunawa, Ma’aikatar Sadarwa ta bayar da sanarwar rufe dukkan layukan da ba su da NIN daga 30 ga Disamba, wanda hakan ya haifar da tururuwar jama’a a ofisoshin NIMC da na layukan sadarwa a dukkan fadin kasar, lamarin da ke haifar da wahalhalu ga al’umma.

Matsalar ta haifar da Majalisar Wakilai ta yi kira ga Bnagaren Zartarwa da ya kara wa’adin rufewar.

SendShareTweetShare
Previous Post

Bikin Kirsimeti: Majalisa Ta Bukaci Ma’aikatar Sufuri Ta Sa Ido Kan Direbobi

Next Post

Nda-Isaiah (1962-2020): An Bada Shaidar Zamansa Jakada Nagari

RelatedPosts

Buba Marwa Ya Zama Sabon Shugaban Hukumar NDLEA

Buba Marwa Ya Zama Sabon Shugaban Hukumar NDLEA

by Nasir S Gwangwazo
9 hours ago
0

Daga Abba Ibrahim Gwale, Shugaban kasa Muhammad Buhari ya amince...

Kananan Hukumomin Jihar Kano

Yau Za A Yi Karon Batta A Zaben Kananan Hukumomin Jihar Kano

by Nasir S Gwangwazo
18 hours ago
0

 Jam’iyyu 11 ne za su fafata PDP Kwankwasiyya ta ce,...

Sojoji

Tsofaffin Sojoji Sun Nemi Karin Kudin Fansho

by Nasir S Gwangwazo
19 hours ago
0

Kungiyar tsofaffin sojoji ta kasa reshen jihar Anambra ta bukaci...

Next Post
Nda-Isaiah (1962-2020)

Nda-Isaiah (1962-2020): An Bada Shaidar Zamansa Jakada Nagari

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version