Idris Aliyu Daudawa">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home KIWON LAFIYA

Gwamnatin Tarayya Ta Kashe Naira Bilyan 1.8 Saboda Yakar Yunwa

by Idris Aliyu Daudawa
January 20, 2021
in KIWON LAFIYA
2 min read
Yakar Yunwa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

A tsakanin 2017 da 2018 gwamnatin Nijeriya ta kashe akalla naira fiye da biliyan 1.8 don ciyar da  kananan yara wadanda suke famma da wahalar matsananciyar yunwa, a  jihohi 18 dake cikn kasar.

Shugaban sashen yaki da kawar da yunwa na ma’aikatar kiwon lafiya Chris Isokpunwu ya sanar da hakan ranar Lahadi, lokacin da yake  hira da Kamfanin dillancin labarai na Nijeriya a Abuja.

samndaads

Isokpunwu ya bayyana cewar sakamakon binciken da ma’aikatar kiwon lafiya ta gudanar a shekarar 2017 ya nuna cewa jihohi 18 a kasarnan na fama da matsananciyar yunwa.

Ya cigaba da bayanin cewar a dalilin haka ne ita gwamnatin ta tsaro matakai tare da hada hannu da Asusun kula da al’amuran gaggawa na kananan yara na majalisar dinkin duniya (UNICEF) domin ganin ta kawo karshen wannan matsala a Nijeriya.

“Daga cikin Naira biliyan 1.8 da gwamnatin tarayyar ta samar da Naira miliyan 600 wanda ma’aikatar kiwon lafiya ta yi amfani da su wajen sayo magungunan, ta waje daya kuma ga kuma shi al’amarin horar da ma’aikata da kuma gina asibitoci.

Ya kara jaddada cewar a shekarar 2018 gwamnati ta kara samar da Naira biliyan 1.2 da hakan ya sa aka samu damar samun damar ciyar da yaran dake fama da matsananciyar yunwa a jihohi 12 na kasar.

Ya cigaba da bayanin cewar, “Da muka gano yawan jihohin dake fama da wannan matsalar a cikin kasar nan sai muka aika masu da wasiku domin sanar da su da matsalar dake tunkarar su da kuma irin taimakon da zamu iya yi masu. Sai dai kuma mun yi rashin sa’a domin kuwa da yawa daga cikin jihohi basu ce mana komai akai ba.”

Ya yi kira da jihohin da su amsa da kiran da ma’aikatar ta yi, bayannan kuma su mai da hankali wajen ganin sun kawar da matsananciyar yunwa wadda yara kanana suke fama da ita.

SendShareTweetShare
Previous Post

Warin Kaji Na Iya Korar Jinsin Sauro Mai Sanya Cutar Maleriya

Next Post

Wadanda Aka Rike Wa Albashi Sun Nemi Gwamna Atiku Ya Duba Matsalarsu

RelatedPosts

Cutar Kyanjamau Ko Sida

Cutar Kyanjamau Ko Sida

by Idris Aliyu Daudawa
21 hours ago
0

Daga Idris Aliyu Daudawa Su kwayoyin cutar sida (da Turanci...

Me Ke Kawo Karkacewar Baki Kwatsam?

Me Ke Kawo Karkacewar Baki Kwatsam?

by Idris Aliyu Daudawa
6 days ago
0

Daga Mustapha Wakili da Muhammad Zahraddin Shanyewar barin fuska larura...

Illolin Shan Ruwa Mai Sanyi Yau Da Gobe

Ruwa Da Amfaninsa A Jikin Dan Adam

by Idris Aliyu Daudawa
7 days ago
0

Amfanin ruwa guda tara a jikin dan Adam idan ya...

Next Post
Gwamna Atiku

Wadanda Aka Rike Wa Albashi Sun Nemi Gwamna Atiku Ya Duba Matsalarsu

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version