Yusuf Shuaibu">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home TATTALIN ARZIKI

Gwamnatin Tarayya Za Ta Biya Ma’aikatan NIMC Albashi Na Musamman – Pantami

by Yusuf Shuaibu
January 28, 2021
in TATTALIN ARZIKI
1 min read
Katin Zama Dan Kasa
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Ministan Sadarwa da Tattalin Arzikin Zamani, Dakta Isa Ali Pantami, ya yi ganawa da shuwagabannin ma’aikatan hukumar kula da katin zaman dan kasa (NIMC), wanda ya amince da bai wa ma’aikataan albashi na musamman bisa karin ayyukan da aka yi musu. Sannan an tattauna sake sabon tsarin biyan ma’aikata da karin girma da kuma biyan sauran hakkokinsu. Pantami ya bukaci hukumar da ta kafa kwamiti na musamman wanda zai bibiyi yadda za a biya albashin na musamman da kuma sauran hakkokin ma’aikatan.

Ministan sadarwa da tattalin arzikin zamani Dakta, Isa Pantami ya bayyana cewa, gwamnatin tarayya tana gudanar da kokari wajen tabbatar da ganin hukumar NIMC ta tsaya da kafafuwanta.
Ya ce, “burin da nake da shi a yanzu shi ne, tabbatar da cewa hukumar NIMC tana samun kudaden shiga da kanta wajen gudanar da ayyukanta ba tare da ta jira kasafi ba daga asusun gwamnatin tarayya.
“Hukumar NIMC yana da matukar mahimmanci wajen bunkasa ci gaban Nijeriya. Zai yi amfani da matsayina na minister wajen bunkasa hukumar,” in ji Pantami.
Gwamnatin tarayya ta bai wa ma’aikatan hukumar wa’adin ranar Jumm’a, 29 ga watan Junairu dukkanin bukatocinsu da kuma sauran abubuwan da suke bukata na gudanar da ayyukansu. Ma’aikatan suna fuskantar rashin isasshen kamfutoci a shalkwatan hukumar da sauran rassan hukumar wanda hakan ke haihar da tsaiko wajen gudanar da ayyukansu yadda ya kamata. Ma’aikatan hukumar NIMC sun roki gwamnatin tarayya da ta yi kokarin cika musu korafe-korafen da suka mika mata domin samun gudanar da ayyukansu yadda ya dace.

samndaads
SendShareTweetShare
Previous Post

Ragin Harajin Shigo Da Motoci Zai Fara Aiki Daga Mako Mai Zuwa

Next Post

Bangaren Gas A Nijeriya Na Cigaba Da Bunkasa – Mele Kyari

RelatedPosts

Farashin Dizel Ya Yi Tashin Gwauron Zabi

Farashin Dizel Ya Yi Tashin Gwauron Zabi

by Yusuf Shuaibu
5 days ago
0

Farashin dizil ya yi tashin gwauron zabi wanda lita daya...

Korona Ta Kawo Tsaikon Kammala Matatar Man Dangote Zuwa 2021

Matatun Man Dangote Za Su karfafa Darajar Naira Da Ceto Tattalin Arziki – Majalisar Wakilai

by Yusuf Shuaibu
5 days ago
0

Majalisar Wakilan Nijeriya ta bayyana cewa, matatan man kamfanin Dangote...

“Duk Da An Sauya Shugabannin Tsaro, Har Yanzu Da Saura”

Na Shirya Tsaf Don Fitar Da Mutum Miliyan 100 Daga Kangin Talauci – Shugaba Buhari

by Yusuf Shuaibu
5 days ago
0

Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya bayyana cewa, burin gwamnatinsa na...

Next Post
Bangaren Gas A Nijeriya Na Cigaba Da Bunkasa – Mele Kyari

Bangaren Gas A Nijeriya Na Cigaba Da Bunkasa – Mele Kyari

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version