Gwamnatin Tarayya Za Ta Daina Ciyar Da Fursunoni Abinci
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Tarayya Za Ta Daina Ciyar Da Fursunoni Abinci

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Gwamnatin Tarayya

Gwamnatin Tarayya za ta dakatar da ciyar da sama da fursunoni 75,507 da ke gidajen yari 244 a kasar nan daga ranar 31 ga watan Disamban 2023 yayin da gwamnatin jihohi kuma ake tsammanin za su fara ciyar da masu laifin a jihohinsu kai tsaye.

Ministan kula da harkokin cikin gida, Ogbeni Rauf Aregbesola, shi ne ya shelanta hakan a jiya sa’ilin da ke kaddamar da shalkwatar hukumar kula da gidajen yari (NCoS) a Owerri da ke Jihar Imo.

  • ‘Yansanda Sun Kama Mutumin Da Ya Kashe Matarsa A Adamawa
  • Gawar Wani Tsoho Mai Shekara 115 Ta Yi Batan Dabo A Anambra

Aregbesola, ya ce, kashi 90 cikin 100 na fursunonin da ake da su, mutane ne da suka yi laifi wa jiharsu, don haka lokaci ya yi da jihohi za su fara zuba kudade su na ciyar da masu laifinsu.

Wannan bayanin na zuwa ne kasa da awa 24 da gwamnatin tarayya ta fito ta ce, tana kashe naira biliyan N22.4 wajen ciyar da fursunoni a fadin kasar nan, kuma har an shigar da hakan cikin kasafin kudin 2023.

Ya hakikance kan cewa matakin zai taimaka wajen rage cinkoson fursunoni a gidajen yarin kasar nan, Aregbesola ya na mai karawa da cewa kaso 80 na fursunoni su na zaman jiran shari’a ne.

Ya ce, akwai bukatar a sake waiwaye sosai kan tsarin shari’a a fadin kasar nan ta yadda za a ke yanke wa masu jiran shari’a hukunci a kan lokaci da daure wadanda suka dace.

A fadinsa, gwamnatin shugaba Buhari ta yi kokari sosai wajen gyara tsare-tsaren tafiyar da gidajen yari ta hanyar kara kudin da ake kashewa, kwaskwarima wa gidajen yari da kuma gina wasu sabbi dukka a kokarin rage yawan cunkoso.

Ministan ya kara da cewa, “Babban kalubalenmu shi ne yawan cinkoson fursunoni a gidajen yari, musamman a biranen da ke da yawan jama’a da yadda mu’amalar jama’a ke karuwa, don haka aikata laifuka zai karu a wannan wajen don haka ne sai ta kai an ajiye wasu a gidajen yari.

“Mun yi kokarin shawo kan wannan matsalar ta hanyar gina manyan gidajen yari guda shida a shiyyoyi shida da suke fadin kasar nan. Na Kano da na Abuja tunin aka kammala su, sauran ma za a kammala.”

Ya nanata cewa akwai gayar bukatar gyara kan tsarin shari’a ta yadda za a yi waiwaye ga dukkanin abubuwan da suke haifar da jinkirin shari’a domin a cewarsa kaso 70 zuwa ma 80 suna zaman jiran shari’a wanda hakan ba daidai ba ne, “Domin na tabbata a wasu lokutan ana tsare wadanda ma basu da laifi a yi ta ajiyesu a gidajen yari, ta hanyar gudanar da shari’a cikin hanzari ne za a gano mai laifi a yanke masa hukunci wanda bai da laifi a sake shi.”

“Wasu kuma koda sun yi laifin, hukuncin da za a yanke musu bai wuce watanni shida ba ya danganta da laifukan da suka aikata. To amma idan ba a yi shari’a ba sai mutum ya shafe tsawon lokaci a tsare.”

“Jihohi su tashi tsaye su gyara sashin shari’arsu su tabbatar ana yanke hukunci a kan lokaci da hanzarin yin shari’a. Wannan zai taimaka sosai wajen wanzar da adalci da kuma kawo karshen zare wanda ake zargi in ya yi laifi kuma a hukunta shi, in bai yi ba a sake shi,” ya shaida.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Next Post
Rayuwar Amina Muhammad, Mataimakiyar Sakatare-Janar Na Majalisar Dinkin Duniya A Takaice

Rayuwar Amina Muhammad, Mataimakiyar Sakatare-Janar Na Majalisar Dinkin Duniya A Takaice

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version