Muhammad Maitela">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Gwamnatin Tarayya Za Ta Gina Kwalejin Kimiyya Ta Farko A Borno

by Muhammad Maitela
January 19, 2021
in LABARAI
2 min read
Kwalejin Kimiyya
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Ranar Litinin Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum ya kai wa ministan ilimi na Nijeriya Malam Adamu

Adamu ziyara tare da godiya, biyo bayan amincewa da shugaban kasa Muhammadu Buhari na gina sabuwar kwalejin kimiyya (Federal Polytechnic) a Monguno, gari mafi yawan jama’a a arewacin jihar Borno, wanda kuma ya dade yana fuskantar koma bayan ilimin boko.

samndaads

Kafin hakan, yau kimanin shekaru 45 da kirkiro jihar Borno (1976), tun a wannan lokacin jihar ta ci gaba da kasancewa daga cikin jihohin yan kadan da basu mallaki kwalejin kimiyya ko kwalejin ilimi ta gwamnatin tarayya ba a fadin kasar nan.

Bugu da kari, kwalejin kimiyya ta Ramat da ke Maiduguri, gwamnatin jihar Borno ce ta gunata kuma take gudanar da ita, wadda a baya jihar ta yi kokarin gwamnatin tarayya ta karbi Ramat Polytechnic amma abin ya ci tura.

Har wala yau kuma, mafi yawan jihohi 36 da ke fadin Nijeriya, kusan kowace za ka tarar tana da daya daga cikin biyun nan- akallah ka sameta da Jami’ar gwamnatin tarayya ko kwalejin kimiyya tare da kwalejin ilimi. Amma ita jihar Borno yau kimanin shekaru 45 da kirkirota amma ba tada ko daya daga dikin wadannan manyan makarantun tarayya, alhalin wasu jihohi da dama da aka kirkiro bayan ta su na kusan duka ukun.

Saboda wannan haki na jihar Borno ya jawo Gwamna Zulum, a matsayin sa na malamin jami’a kuma tsohon shugaban Ramat Polytechnic, ya tashi tsaye haikan wajen bin bayan wannan matsala a wajen gwamnatin tarayya domin gina sabbin kwalejin kimiyya da kwalejin ilimi a jihar Borno, duk da halin da ake ciki ta matsalar rikicin Boko Haram, wadda za a gina a arewacin jihar.

Wanda bisa ga hakan ne Farfesa Zulum ya bayyana farincikin sa a sa’ilin ziyarar da ya kaiwa ministan ilimin a sakatariyar gwamnatin tarayya da ke Abuja. Yayin da ya yaba wa gwamnatin shugaban kasa Buhari dangane da amincewa da gina sabuwar kwalejin tare da bika dimbin godiya ga ministan ilimi Malam Adamu Adamu bisa tabbatar da umurnin da nuna kauna ga al’ummar jihar Borno.

A nashi bangaren, minista Adamu ya sanar wa Gwamna Zulum cewa baya ga gina sabuwar kwalejin kimiyya, nan kusa kuma Borno za ta samu karin kwalejin ilimi kamar yadda yake a mafi yawan jihohin kasar nan 36.

SendShareTweetShare
Previous Post

Hatsarin Motar Argungu: Bakwai Sun Rasu, Sama Da 30 Sun Jikkata

Next Post

Korona: Har Yanzu Babu Ranar Bude Makarantu A Jihar Kaduna

RelatedPosts

Matsalar Tsaro: Wainar Da Aka Toya A Taron Gwamnoni Da Sarakunan Arewa

Matsalar Tsaro: Wainar Da Aka Toya A Taron Gwamnoni Da Sarakunan Arewa

by Muhammad Maitela
13 hours ago
0

Daga Ibrahim Ibrahim, Kaduna A jiya Alhamis ne masu ruwa...

‘Yan Bindiga Sun Sace Dalibai Mata 300 A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Sace Dalibai Mata 300 A Zamfara

by Muhammad Maitela
15 hours ago
0

Rahotanni daga jihar Zamfara na cewa 'yan bindiga sun kai...

Yadda ‘Yan Kungiyar Asiri Suka Tayar Da Hankulan Jama’a A Lokoja

Yadda ‘Yan Kungiyar Asiri Suka Tayar Da Hankulan Jama’a A Lokoja

by Muhammad Maitela
16 hours ago
0

Daga Ahmed Muhammed Danasabe, Lokoja Mazauna birnin Lokoja da kewayenta,...

Next Post
Ranar Bude Makarantu

Korona: Har Yanzu Babu Ranar Bude Makarantu A Jihar Kaduna

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version