Gwamnatin Zamfara Ta Kaddamar Da Gangamin Kula Da Lafiya Kyauta
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnatin Zamfara Ta Kaddamar Da Gangamin Kula Da Lafiya Kyauta

byHussein Yero
2 years ago
Zamfara

Gwamnatin Jihar Zamfara ta ƙaddamar da babban gangamin duba marasa lafiya kyauta, wanda zai magance wasu cututtuka da suke addabar al’umma.

Sashe na farko na wannan shiri an fara shi ne da haɗin gwiwa da ofishin matar gwamnan jihar, Hajiya Huriyya Dauda Lawal, wanda zai taimakawa mutanen da ke fama da cutar yanar ido (cataract), cutar gwaiwa (groin swellings), cutar yoyon fitsari (VVF) da kuma ilimin yadda za su kiwata lafiyarsu.

  • Yadda Tawagar Malaman Nijeriya Suka Tattauna Da Sojojin Juyin Mulkin Nijar

 

Wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sulaiman Bala Idris, ya fitar a ranar Lahadi, ta ce wannan gangami na kula da kiwon lafiya kyauta an fara shi ne ranar Juma’ar da ta gabata, inda aka samu nasarar yi wa mutum 81 aikin ido, da kuma yi wa mutum 49 aikin cutar gwaiwa.

Ya ƙara da cewa, wannan babban gangami na kiwon lafiya an tsara duk wata zai yi aiki ga masu cutar gwaiwa mutum 1, 000, za a kuma yi wa mata 200 masu fama da yoyon fitsairi aiki, haka nan za a yi aiki ga mutum 1, 000 masu fama da ciwon ido.

Sanarwar ta ce: “Gwamnatin Zamfara ta kafa kwamiti ne na ƙwararru waɗanda suka yi bincike suka tsamo nau’ikan cututtukan da ke addabar mutane.

“Binciken kwamitin ne ya tabbatar da cewa, mutane sun fi buƙatar aiki kyauta a cututtuka irinsu yanar ido, cutar gwaiwa, cutar yoyon fitsari da ilimin yadda za su kiwata lafiyarsu.

“Wannan shi ne karo na farko a Jihar Zamfara da gwamnati take yin gangami don kula da kiwon lafiyar jama’a masu fama da manyan cututtuka.

“Wannan gangami ya bayar da dama ga dukkanin ‘yan jiha daga kauyuka da birane don su amfana.

“Wannan yana daga cikin ƙoƙarin gwamnatin Dauda Lawal na tabbatar da yi wa sashen kiwon lafiya garanbawul. Kuma wannan gangami na bayar da tallafin ana bada shi ne ga dukkanin jama’ar da ke ƙananan hukumomi 14.

“Ana yin wannan gangami ne a babban asibitin Gusau, babban asibitin Sarki Fahad, da kuma Asibitin Kwararru na Yariman Bakura.” In ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Tottenham Na Neman Gift Orban Na Gent Domin Maye Gurbin Kane

Tottenham Na Neman Gift Orban Na Gent Domin Maye Gurbin Kane

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version