Gwamnonin PDP Sun Caccaki Gwamnatin Tarayya Kan Tsadar Rayuwa
  • English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Gwamnonin PDP Sun Caccaki Gwamnatin Tarayya Kan Tsadar Rayuwa

byYusuf Shuaibu
2 years ago
PDP

Kungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP sun caccaki gwamnatin tarayya kan matsin rayuwa tare da yin kira ta kawo matakan gaggawa da za su kawar da matsalar tattalin arziki da kalubalan tsaro da ke addabar kasar nan.

Shugaban kungiyar gwamnonin PDP kuma gwamnan Jihar Bauchi, Bala Mohammed shi ya yi wannan kira lokacin da yake zantawa da manema labarai jim kadan bayan kammala ganawar gwamnonin jam’iyyar adawa da ya gudana a gidan gwamnatin Jihar Oyo da ke Abuja.

  • Nijeriya Za Ta Shawo Kan Ƙalubalen Da Take Fuskanta Nan Gaba Kaɗan – Ganduje
  • Shugaba Tinubu Ya Gana Da Gwamnoni Kan Ƙalubalen Da Nijeriya Ke Fuskanta

Da yake amsa tambayoyi kan tsadar rayuwa da ake ciki, gwamnan ya bayyana cewa sun goyi bayan cire tallafin man fetur da wannan gwamnati ta yi ne bisa fatan za a samu saukin rayuwa, amma lamarin ba haka yake ba.

Ya bayyana damuwarsa kan yadda darajar naira ke kara zubewa kasa warwar, yayin da ake ci gaba da samun tsadar rayuwa.

A cewarsa, “Lallai muna caccakan munanan manufofin gwamnatin tarayya. Amma a bangare daya kuma, mun goyi bayan wannan gwamnati na cire tallafin mai, saboda muna da tabbacin cewa hakan shi ne manufa, idan har muka hada kai, to za a samu mafita kan wannan lamari.

“Amma muna ganin shi ne ya kawo faduwar daragar naira wanda ya haddasa tsadar rayuwa, inda a yanzu muke kafada da kafada da kasar Benezuela.

Saboda haka, muna hamayya da munanan manufofin gwamnatin tarayya ba tare da mun zagi kowa ba.

“Mun dauki wannan mataki ne domin ceto ‘yan Nijeriya da kuma kasar nan ta yadda za mu yi wasu abubuwa domin taimaka wa kawunanmu.”

Tun da farko, kungiyar ta jaddata manufarta na kirkiran ‘yansandar jihohi a matsayin wani taki da zai kawo karshen matsalar tsaro a Nijeriya.

“Wannan tattaunawar ta shafi sake duba yadda kasa ke ciki da kuma matsin rayuwa da ‘yan Nijeriya suka tsinci kansu a ciki sakamakon matsin tattalin arziki da kalubalan tsaro da kasar ke fuskanta. Wannan kungiyarmu tana kira ga gwamnatin tarayya ta bullo da wasu shirye-shirye da zai kunshi dukkanin gwamnatocin kasar nan domin kawo karshen lamarin.

“Gwamnonin PDP za su ci gaba da yin iya bakin kokarinsu wajen kawo karshen matsalar tsaro domin bayar da kariya ga al’ummar kasar nan. Muna jaddada aniyarmu na yin kira da a kirkiro ‘yansandar jihohi domin kaucewa duk wata hanya ta yin amfani da ofishi ba bisa ka’ida ba ga bangarorin gwamnati.

“Lallain kungiyarmu ta koka kan yadda darajar naira ya karye tare da yinkira ga hukumomin kula da kudade da su ballo da mafita,” in ji kungiyar gwamnonin PDP.

Gwamnonin PDP sun amince da kwamitin gudanarwar jam’iyyar na kasakarkashin jagorancin mukaddasin shugaban jam’iyyar na kasa, Umar Damagum. Haka kuma sun bukaci kwamitin ya kira taron gaggawa na k asa ba da jimawa ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Umarci Dukkan Mambobinta Su Yi Murabus Daga Tsoffin Jam’iyyunsu

October 3, 2025
Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar
Tambarin Dimokuradiyya

Dage Zaben Shugabannin PDP Na Jihohi Ya Kara Ruruta Wutar Rikici A Jam’iyyar

October 3, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan
Tambarin Dimokuradiyya

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Next Post
Za Mu Taimaka PDP Ta Fadi Zaben 2023 -Wike

Wike Zai Sake Kwace Filaye Da Dama A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version