Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home RIGAR 'YANCI

Gwanmatin Kano Ta Yi Rawar Gani A Kaddamar Da Littafin Salatin Annabi – Nuhu Gudaji

by Muhammad
February 23, 2021
in RIGAR 'YANCI
2 min read
Littafin
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Daga Mustapha Ibrahim,

Taron bakin kadamar da litafin sallatin Annabi Muhammad Sallallahu a Alaihi wasallam ya yi armashi kuma Gwamnatin jihar Kano a karkashin jagorancin Dr Abdullahi Umar Ganduje da Masarautar Kano bisa jagorancin Mai martaba Sarkin Kano, Alhaji Aminu Ado Bayero, da sauran sarakuna daga masarautar Bichi, Rano, Karaye da Gaya da asttajiran Kano irinsu Alhaji Kabiru Sani Kwangila da ’yan siyasa irinsu shugaban karamar hukumar birnin Kano, Hon. Hafiz Alfindiki, sun yi rawar gani wajen samun gagarumar nasara a wannan biki na kadamar da litafin da Malama Hajara Muhammad Kabir ta walafa a wannan lokaci.

Bayanin haka ya fito ne daga bakin shugaban Kwamitin aiwatar da taron kaddamar da littafin, Malam Nuhu Gudaji, a zantawarsu da wakilinmu ta wayar tarho bayan kammala taron, wanda aka yi a ranar Asabar da ta gabata a harabar Masarautar Kano dake Kofar Kudu a karamar hukumar birnin Kano.

Har ila yau ya ce, yadda Gwamnan Kano, Dr. Abdullahi Umar Ganduje, ya kaddamar da littafin akan kudi Naira Miliyan guda bisa wakilcin Sakataren Gwamnati kuma Wazirin Masarautar Gaya, Alhaji Usman Alhaji, abun a yaba ne ganin yadda Gwamnatin Kano ta ba wa abun mahimanci.

“Duk wannan sun cancanci yabo da sauran al`uma da suka fanshi litafin akan farashi daban-daban da ma sauran al’umma da suka bada gudunmawa wajen samun nasarar bikin kaddamar da littafin na Malama Hajara Muhammad Kabir.”

A nata takaitacen jawabin godiya da ta yi Malama Hajara ta bayyana makasudin wannan littafi, inda ta ce domin zaburar da matasa da yara maza da mata sanin muhimmancin salatin Annabi Alhis salam da kuma riko da shi, domin samun tsira a duniya da lahira inda kuma ta yi godiya ga Gwamnan Jihar Kano da daukacin shugabanni da sarakuna da sauran al’umma bisa gagarumar gudunmawa da hadin kai da al’umma ta bayar a wannan muhimmin taro.

SendShareTweetShare
Previous Post

Sarkin Zuru Adalin Sarki Ne – Wakilin Zurun Igabi

Next Post

Akwai Bukatar Ba Wa Matasa Dama Mai Yawa A Gwamnati – Sardaunan Matasa

RelatedPosts

Ma’aikatar Yada Labaran Kano Na Hada Hannu Domin Tunkarar Kalubalen Abinci Marasa Gina Jiki

Ma’aikatar Yada Labaran Kano Na Hada Hannu Domin Tunkarar Kalubalen Abinci Marasa Gina Jiki

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Daga Abdullahi Muhammad Sheka, Kano   Ma’aikatar yada labaran Jihar...

Bilya Bawale

Bilya Bawale Ya Zamo Sardaunan Matasan Kabi Na Farko

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Daga Jamil Gulma, Birnin Kebbi   Masarautar Kabin Argungu da...

Garun Danga

Karamar Hukumar Gabasawa Gidan APC Ce – Garun Danga

by Sulaiman Ibrahim
1 day ago
0

Daga Ibrahim Muhammad, Kano   Shugaban Karamar Hukumar Gabasawa, Hon....

Next Post
Gwamnati

Akwai Bukatar Ba Wa Matasa Dama Mai Yawa A Gwamnati – Sardaunan Matasa

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version