Yusuf Shuaibu">
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home TATTALIN ARZIKI

Gyara Matatun Mai Kadai Hanyar Farfado Da Tattalin Arziki – Tsohon Daraktan CBN

by Yusuf Shuaibu
January 4, 2021
in TATTALIN ARZIKI
1 min read
Matatar Mai
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Tsohon daratan sashin kasafin kudade a Babban Bankin Nijeriya (CBN), Dakta Titus Okunrounmu ya bukaci gwamnatin tarayya  da mayar da hankali wajen kokarin gyara matatun kasar nan, domin gyara matatun kasar nan ne kadai hanyar farfado da tattalin arziki a shekarar 2021. Okunrounmu ya yi wannan kira ne lokacin da yake zantawa da manema labarai a garin Ota da ke cikin Jihar Ogun.

Ya ce, “akwai bukatar kasar nan ta sake gina matatun mai tare da gyara matatun man da ake da su, idan ana son farfado da tattalin arziki a shekarar 2021,” in ji shi.

samndaads

Ya kara da cewa, babu wata kasa da take sayar da danyan mai a kasuwan duniya kuma ta zuwa tana siyo man da aka tace a kasashen ketare sai dai kasar Nijeriya. Ya ce, ya kamata kasar nan ta daina shigo da mai ta yi kokarin gyara matatun mai wanda zai sa a dunga zuwa Nijeriya ana sayan tataccen mai. Tsohon daraktan ya ce, bayar haka kuma, yana da matukar mahimmanci a wadata ‘yan kasa da tataccen  man fetur ta yadda za a samu nasarar samun karin kudaden shiga masu yawan gaske. Ya kara jaddada cewa, idan ana tace man a Nijeriya, za a samu damar fitar da wasu man zuwa kasashen ketare kamar irin su man jirgi da man inji da dai sauran su, sannan kuma har ila yau za a ci gaba da fitar da man fetur din a sauran kasashe da ke fidin duniya, wanda zai kara sa Nijeriya ta ci gaba da gudanar da harkokin kasuwanci da sauran kasashe tare da samun kudaden shiga masu yawa marasa adadi. Ya ce, matukar gwamnatin tarayya ba ta dauki matakin daina shigowa da mai kasar nan ba, to zai yi wahala a sami wani canji a bangaren tattalin arziki a shekarar 2021.

SendShareTweetShare
Previous Post

Ndume Ya Kaddamar Da Rabon Tallafin Jari Ga Mata A Kudancin Borno

Next Post

An Nuna Bukatar Kawo Karshen Talauci A 2021 A Nijeriya

RelatedPosts

Kangin Talauci

Shirin Tsamo Mutane Miliyan Biyu Daga Kangin Talauci Ya Kankama – Osinbajo

by Yusuf Shuaibu
3 days ago
0

Bayan samun nasarar kaddamar da shirin farfado da tattalin arziki...

Talakawan Nijeriya

Talakawan Nijeriya Miliyan 24.3 Sun Samu Tallafin Naira 5,000 Kowanne – Ministar Jinkai

by Yusuf Shuaibu
3 days ago
0

A ranar Talata ne, gwamnatin tarayya ta bayyana cewa, sama...

FIRS

FIRS Ta Tattara Harajin Tiriliyan N4.9 A Shekarar 2020 Duk Da Korona

by Yusuf Shuaibu
4 days ago
0

Hukumar tattara haraji ta kasa (FIRS) ta bayyana cewa, ta...

Next Post
Gidauniyar Zarah And Arthur

An Nuna Bukatar Kawo Karshen Talauci A 2021 A Nijeriya

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version