Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
No Result
View All Result
Leadership Hausa Newspapers
No Result
View All Result
Home LABARAI

Hajjin Bana: Likitoci Sun Duba Alhazan Jigawa 2,300 A Saudiyya

by Tayo Adelaja
September 14, 2017
in LABARAI
2 min read
WhatsAppShare on FacebookShare on TwitterShare on Telegram

Munkaila T. Abdullah, Daga Makkah

Kimanin Alhazai sama da dubu 2,000 ne daga Jihar Jigawa wadanda ke fama da rashin lafiya daban-daban, likitoci suka duba a cikin makwanni biyu a yayin zamansu a kasa mai tsarki domin gudanar da aikin hajji a wannan shekara ta 2017.

samndaads

Shugaban tawargar likitocin Jihar ta Jigawa a aikin hajjin na bana, Dakta Ibrahim Mika’il ne ya shaidawa wakilinmu a yayin zantawarsu jiya a Birnin Makkah.

Daktan ya bayyana cewa, ‎daga fara aikin hajjin na bana zuwa yanzu, tawagar tasu ta likitoci ta yi nasarar duba kimanin Mahajjatan Jigawa Dubu 2,300 a cikin makwanni uku da suka gabata, tun daga saukarsu a birnin Madina, zaman Minna, Arafa da kuma zamansu a birnin Makkah bayan kammala aikin hajjin na bana.

Shugaban ya kuma bayyana cewa, duk da kasancewar ba a samu rahoton rasuwar wani Maniyyaci ko daya daga Jihar Jigawa ba, amma an samu yawaitar rashin lafiya akai-akai.

Dakta Mika’il ya ce, mafi yawancin cututtukan da suka fi addabar mahajjatan sun hada da cutar zazzabi, zazzabin mura, cutar gyambon ciki da kuma‎ lalacewar ciki sakamakon sauyin yanayi da aka tsinci kai a ciki.

Sannan kuma ya ce, cikin mutane 39 kuwa da aka aike dasu zuwa manyan asibitocin Hukumar Alhazai ta Kasa da kuma Babban Asibitin Sarki Abdul’Aziz, wasunsu sun samu matsala‎r karaya da kuma cutar Sikila gami da sauran cututtuka masu zafin gaske.

Babban Likitan, ya kuma shawarci Alhazan da su kiyaye irin hadin gambizar abincin da zasu ci gami da tsaftace muhallin da suka zaune domin samun saukin yaduwar ire-iren wadannan cututtuka a yayin zaman ragowar kwanakin nasu a kasa mai tsarki.

Daga karshe shugaban likitocin ya kuma yaba wa gwamnan jihar ta Jigawa Alhaji Muhammad Abubakar Badara bisa cikakken goyon bayan da ya baiwa tawagar tasa domin tabbatarda Alhazan na Jigawa sun kammala aikin hajjinsu cikin koshin lafiya.

SendShareTweetShare
Previous Post

Farfesa Bashar Aliero Ya Zama Sabon Shugaban Jami’ar Kimiyya da Fasaha Ta Kebbi

Next Post

Gwamnatin Sakkwato Za Ta Sayar Da Gidajen Gwamnati 1,500

RelatedPosts

Za A Kulle Duk Layin Da Ba A Yi Rijistarsa Da Katin Dan Kasa Ba Ranar 9 Ga Fabrairu

Za A Kulle Duk Layin Da Ba A Yi Rijistarsa Da Katin Dan Kasa Ba Ranar 9 Ga Fabrairu

by Sulaiman Ibrahim
11 hours ago
0

Gwamnatin Tarayya ta kara wa’adin da aka diba wa ’yan...

Sayar Da Kadarorin Gwamnati Zai Taimaki ‘Yan Nijeriya, Inji Minista

Sayar Da Kadarorin Gwamnati Zai Taimaki ‘Yan Nijeriya, Inji Minista

by Sulaiman Ibrahim
11 hours ago
0

Ministar Kudi, Zainab Ahmed, ayau Juma’a, ta ce shirin Gwamnatin...

Zakzaky

Matar Sheikh EL-Zakzaky Ta Kamu Da Korona, In Ji Danta

by Muhammad
16 hours ago
0

Daga Rabiu Ali Indabawa, Matar Shugaban Kungiyar Musulunci a Nijeriya...

Next Post

Gwamnatin Sakkwato Za Ta Sayar Da Gidajen Gwamnati 1,500

Leave a Reply Cancel reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Domin sanya talla ko karin bayani a tuntube wannan numbar +2348126152609.

Leadership Epaper
ADVERTISEMENT
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU
Advertise with us

© 2020 Leadership Group .

No Result
View All Result
  • LABARAI
  • WASANNI
  • RAHOTANNI
  • SIYASA
  • KASUWANCI
  • ADABI
  • RA’AYINMU
  • TATTAUNAWA
  • BIDIYO
  • MAKALAR YAU

© 2020 Leadership Group .

Go to mobile version