Har Yanzu Ba Labari: Awanni 48 Bayan Sace Ƴan Jarida Da Iyalansu A Kaduna
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Ba Labari: Awanni 48 Bayan Sace Ƴan Jarida Da Iyalansu A Kaduna

byAbubakar Sulaiman
1 year ago
Labari

Awanni 48 bayan sace ƴan jarida biyu da iyalansu a Jihar Kaduna, har yanzu ba a san inda suke ba. ‘Yan bindiga sun kutsa cikin unguwar Danhonu a Millennium City, ƙaramar hukumar Chikun, inda suka kai hari gidajen AbdulGafar Alabelewe na jaridar The Nation da AbdulRaheem Aodu na jaridar Blueprint, suka sace su tare da matansu da ‘ya’yansu. An sako matar AbdulRaheem daga baya saboda rashin iya bin masu sacewa sakamakon rashin lafiya.

Ɗan uwa ga ɗaya daga cikin waɗanda aka sace, Taofeeq Olayemi, ya bayyana damuwar da iyalan suke ciki, yana mai cewa ba su samu wata alaƙa da ‘yan uwan da aka sace ba tun bayan faruwar lamarin ba. Ya ce, “Wannan lokaci ne mai matuƙar wahala ga iyalan saboda ba mu san halin da suke ciki ba kuma ba mu san inda suke ba. Muna ta addu’a ga Allah ya kiyaye su kuma ya sassauta zuciyar waɗanda suka sace su.”

  • Ƴancin Ƙananan Hukumomi Zai Taimaka Wajen Magance Matsalolin Tsaro – COAS
  • Atiku Ya Koka Kan Yadda Matsalar Tsaro Ta Addabi ‘Yan Nijeriya

Kakakin rundunar ‘yan sanda (PPRO) a Kaduna, ASP Mansir Hassan, ya ce jami’an tsaro suna iyakar kokarinsu don ganin sun kuɓutar da waɗanda aka sace ba tare da wani rauni ba. Ya bayyana cewa an tura jami’ai cikin dajin da ake zaton ‘yan bindigar suke buya.

Ƙungiyar ‘Yan Jaridu ta Najeriya (NUJ) a Kaduna ta yi tir da wannan sacewa a cikin wata sanarwa da shugaban ƙungiyar, Comrade Asmau Yawo Halilu, da Sakataren ƙungiyar, Comrade Gambo Santos Sanga, suka sanya wa hannu. Sun roƙi hukumomin tsaro da su ɗauki matakin gaggawa don ceto ‘yan jaridar da iyalansu.

Kungiyar Arewa Youth Consultative Forum (AYCF) ta yi Allah wadai da garkuwar da aka yi da ƴan jaridar. Shugaban ƙungiyar, Alhaji Yerima Shettima, ya yi kira ga hukumomin gwamnati da na tsaro su ƙara kokari don ganin an sako waɗanda aka sace lafiya kuma a kawo karshen irin waɗannan munanan al’amura. Ya kuma bukaci jama’a su yi addu’a don ganin an sako waɗanda aka sace lafiya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
Ba Samar Da Damar Samun Ci Gaba Kawai Ke Sa Kasar Sin Samun Karbuwa Ba

Ba Samar Da Damar Samun Ci Gaba Kawai Ke Sa Kasar Sin Samun Karbuwa Ba

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version