Har Yanzu Ina Fuskantar Matsala Saboda Shigowata Harkar Fim —Saratu Abubakar
  • English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Har Yanzu Ina Fuskantar Matsala Saboda Shigowata Harkar Fim —Saratu Abubakar

byBello Hamza
3 years ago
Saratu

Sabuwar jaruma a masana’antar finafinai ta Kannywood, ta bayyana shigowar ta masana’antar da cewa lokacin ta ne ya yi don haka ba ta yi mamaki ba da ta kasance cikin wadanda a ke damawa da su a cikin harkar, saboda yadda ta dade ta na son ta yi tun ta na karama don haka sai a yanzu ne ta samu cikar burin ta na zama ‘yar fim.

Jarumar ta bayyana hakan ne a lokacin tattaunawar mu da ita Inda take cewa, “Tsawon lokacin da na yi ina fatan na kasance ‘yar fim sai a yanzu na cika burina wanda a yanzu duk da ban dade da shigowa ba, don na fara ne a 2020 in da na fara fitowa a fim din ‘Hajiya Babba’ da ‘Ya’yan Mage’, kuma a yanzu ni ce jarumar fim din ‘Zo Mu Zauna’, kuma ina jin dadi sosai da hakan’.

  • ‘Yan Kannywood Mu Guji Isar Da Sakon Da Bai Dace Ba -Yunusa Gaya

Dangane da ko ta samu matsala daga gidan su a lokacin da ta shigo kuwa cewa ta yi, “Ai matsala sosai ma kuwa don har yanzu ina fuskantar matsalar, saboda ka san shi fim a nan kasar mu ta Hausa idan mutum ya na yi sai a rinka cewa shi dan iska ne.

To wannan ta sa har gida aka je a ke samun iyaye na ana cewa sun bar ni ina iskanci har abin ya yi musu yawa su ke ta mini magana, don haka sai nake fada musu cewa ni fa a rayuwa ta ba zan yi abin da bai dace ba, ni na san din sana’a ce kuma ita ta kawo ni, neman kudi nake yi, kuma ba wai zaman banza nake yi ba a Kano karatu nake yi sai kuma nake hadawa da fim saboda sana’a ce, don haka ba iskanci nake yi ba na dauke shi a matsayin sana’a da zan rinka yi ina rufawa kaina asiri, to haka dai suka yarda suka hakura tunda ya za su yi da ni, tunda ina cikin fim din na shiga dumu-dumu, kawai dai sai wani lokacin idan na je gida za a ce shikenan dai na shiga harkar fim ba zan yi aure ba.

Na Kano ce musu aure lokaci ne idan Allah ya kawo za a yi.”
Dangane da fim din da ta fito a matsayin Jaruma kuwa wato zo mu zauna cewa ta yi ‘Ina alfahari da fim din, domin shi ne ya fito da ni duniya ta san da ni kuma matsayin da aka ba ni na babbar Mace ya zo mini da bazata, saboda a matsayina na Budurwa da ban taba yin aure ba sai ga shi a fim na kasance matar aure har da babbar ‘ya da zan aurar da ita.

Wannan matsayin ya daga daraja ta sai na zo ina jin kaina kamar matar aure ka ga wannan ai daukaka ce, don haka a kullum ina alfahari da fim din ‘Zo Mu Zauna.”

A game da mu’amalarta da mutane kuwa cewa ta yi ta samu ce gaba sosai.”Domin duk lokacin da na je gida, sai ka ga duk wajen da na shiga a na ta zuwa wajena don ma ba ko’ina nake shiga ba saboda duk in da ka je za a ta kallon ka”.

A game da yadda mu’amalarta take kasancewa da masoyanta kuwa cewa ta yi abin ya na burge ta saboda “Duk in da na je a na zuwa a dauki hoto da ni kuma ina samun kyauta daga wajen masoyana sannan kuma idan na shiga cikin ‘yan fim mu kan zama kamar ‘yan’uwa don ba na gane ma ba a gida nake ba saboda an hadu an zama daya, haka a ke zama a yi wasa da dariya, don yau idan ba ni da lafiya na san wanda zan kira a cikin ‘yan fim ya tsaya a kaina.

Don haka muna zama ne kamar ‘yan uwan juna.”
Daga karshe ta yi kira ga jama’a da su daina yi wa ‘yan fim kallon ‘yan iska, saboda ba kowa ba ne dan iska, don akwai mutane nagari kamar kowacce harkar, da mutanen kirki da na banza, to haka ma harkar fim take. Inji Saratu Abubakar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano
Nishadi

Kotu Ta Aike Da Ɗan TikTok Gidan Gyaran Hali Kan Bidiyon Batsa A Kano

October 6, 2025
An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana
Nishadi

An Nada Adamar Kamaye Sarautar Jakadiya A Kasar Ghana

October 4, 2025
Daga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa
Nishadi

Daga Kallon Fina-finan Indiya Na Samu Sha’awar Fadawa Kannywood – Kamalu Mijinyawa

September 28, 2025
Next Post
Kungiyar SCO Na Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya

Kungiyar SCO Na Tabbatar Da Zaman Lafiya A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Exit mobile version